HUDUBAR
JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN-ZARIA
Watan Sha’aban; Jakadan Ramadan-Daga Bakin Imam Sheikh S. S
Abubakar
A’udhu BilLahi minas Shaidan Ar-Rajim,
BismilLahir Rahman
Ar-Raheem,
Godiya sun tabbata ga Allah,
muna yabo gare sa Madaukakin Sarki. Muna shaidawa lallai babu abin bauta da
gaskiya face Allah shi kadai ya ke wanda ya shar’anta ga Bayin sa tafarkin da
zai kai ga samun yardar Sa.
Muna shaidawa lallai Shugaban mu; Annabi Muhammad SAW Bawan Allah ne kuma
Manzon Sa, wanda ya shiryar
da Al’ummar sa ga yin biyayya ga sunnar sa.
Bayan haka:
‘Yan uwa a yau muna cikin
rana ta farko na Watan Sha’aban wanda Manzon Allah SAW ya kasance yana damuwa
da shi saboda abin da aka ruwaito daga Usama Dan Zaid RA, yace: Na ce da Manzon
Allah SAW meyasa yake azumi a cikin Watanni amma ba kamar yadda yake yin azumi
a Watan Sha’aban ba? Sai
Manzo SAW yace: “Saboda
wannan wata ne da Mutane su ke rafkana da shi wanda yake tsakanin Rajab da kuma
Ramadan kuma wata ne wanda a cikin sa ana daukaka ayyuka zuwa ga Allah, sannan Ni ina so
a daukaka ayyuka na ina mai azumi.” Imam Al-Nisa’i ya ruwaito wannan Hadisi kuma Malaman
Hadisi sun inganta shi.
Kenan Annabi SAW yana son
Azumi a cikin wannan wata saboda a cikin sa ake daukaka aiki a gaban Allah
Madaukaki inda yake so a bayyana ayyukan sa yana mai azumi. Wannan wata dai shi
ne
Jakadan mai martaba wanda yake zuwa kafin abin so mai girma da daraja. Shi dai wannan
wata Sha’aban shi ne Jakada na watan Ramadan abin son mu. Kuma wannan zai
kasance ne ta hanyar aikata al’amura masu sauki ga wanda shi damuwar sa ya samu
yalwa da haske a cikin kabarin sa bayan mutuwa. Kuma abubuwa ne da Mutum zai
gabatar idan har manufar sa ya samu jin kai da yardar Ubangiji SWT, wanda ya
kasance haka ne tunanin sa zai yi kokari ya girmama Jakada ga watan Ramadan.
Ta yaya ake girmama wannan Watan? Ta yin Azumi a cikin sa
kamar yadda Hadisi ya gabata da kuma abin da aka ruwaito daga Aisha RA inda ta
ke cewa: Ni, ban ga Annabi SAW yana cika Azumi wani Wata in ba Ramadan ba, amma
kuma ban taba ganin Watan da yake yawaita Azumi ba kamar Watar Sha’aban. A wata
ruwayar Nana A’isha RA ta ke cewa Manzo SAW yana azumtar daukacin Watan. Don
haka ya kamata muyi kwaikwayo da wannan Sunnah na yawaita Azumi domin karrama
wannan Wata.
Abu na biyu da za muyi domin karrama wannan Watan da yake
Jakada na Ramadan shi ne mu tsarkake rayuwakan mu daga abubuwa na zunubi da
kuma sabon Allah. Gidajen mu su tsabtatu daga duk wata kazanta. Sannan kuma a
kula da tuba Bayin Allah; tuba ta nasiha zuwa ga Allah. Mu kuma yi kokari mu ga
abin da zai zama sulhu tsakanin mu da Mahallicin mu; mu bude wani sabon farin
shafi ga abin da yayi saura na rayuwar mu kuma kullum mu rika jin albishir da
cewa Allah zai yafe mana idan mu ka nemi ya yafe kana ya karbi tuba ba tare da
cire tsammani ba, kamar yadda aka fada a
Al-Kur’ani cewa ka da a yanke tsammani daga gafarar Ubangiji don lallai Allah
yana yafe zunubai baki daya domin shi mai yawan gafara ne da jin kai.
Saboda haka ‘Yan uwa Musulmi sai duk mu yawaita kwadayi
na cewa ka da Watan Ramadan ya shigo mana face cewa muna cikin tsarki da tsabta
a wannan Wata da za muyi tattali. Sai mu kiyayi wani abu na shirka wanda Allah
SWT yayi alkawari ba zai yafewa duk wanda ya mutu yana kai ba. Shirka dai abu
ne da ya zama ruwan dare a yau, Jama’a na rayuwa cikin Mutane da yawa ba tare
da sanin haka ba. Dole ne ayi kokarin kaucewa Shirka. Mu’amular da Jama’a ke yi
na jefa su hannuwan Bokaye masu yi masu alkawari na banza su na nuna masu cewa
za su yi masu abubuwan da babu mai yin su sai Allah Sarki. Haka kuma ga Shirka
ta riya da ta ke bayyana wanda Mutum ba zai aikata alheri ba sai dai don a gani
a yaba. Wannan duk ya kamata mu kaurace masu.
Sannan kuma mu kiyayi zalunci duk irin zalunci da Shari’a
ta fada don ba shi da rana. Kamar yadda ba za mu so a zalunci namu ba, don
Allah ya fada da kan sa cewa shi ya haramtawa kan sa zalunci, don haka mu ma ka
da mu yi zalunci mu nisance sa kamar yadda Shari’a ta fada. Sannan kuma ya kai
wanda hakkokan Mutane ya ke gare ka, ka tabbatar cewa ka da ka tare hakkin wani
ko har wani yayi kuka da kai. Wannan yana cikin aikin zalunci wanda bai dace
duk wani mai jiran Rahamar Allah SWT yayi ba.
Ya kai wanda ka ke kangarewa ga Mahaifan ka, ya kamata ka
nemi yardar Allah SWT ta kofofin da ake samun yarda. Daga cikin wadannan kofofi
akwai hanyar biyayya ga Iyaye. Saboda haka idan kana da iyaye kuma har Allah ya
hada ka zama da su. Ka yi kokari ka samu yardar su don biyayya gare su wajibi
ne idan har bai saba fushin Allah ba. Fushin Allah kuma yana ga fushin Mahaifa
idan har sun yi bisa ga abin da su ke da hakki a kai.
Girmamawa na uku da za muyi wa wancan Wata shi ne mu
yawaita karatun Al-Kur’ani. Hakika wadanda su ke magabata kuma managarta shugannin
mu su na iya bakin kokari na tattali domin shiga cikin Watan Ramadan. Ga duk wanda
ya san irin falalar Watan Ramadan ba zai yarda cewa sai ta shigo kafin ya fara
azumi ba watau tattalin abin cin riba na Watan. Wanda yake Dan kasuwa mai
hangen nesa zai yi tattali ne tun kafin Ranar kasuwa ya ci riba, ba sai Ranar
ne zai nemi kayan da zai sayo sannan ya saida ba. Don haka dai komai yana
bukatar shiri; Magabatan mu kan yi shirin ne domin cin ribar Watan Ramadan. Ba
su kyale Duniya ta rude su har su shantake ba wanda Duniya mai yawan yaudara ce
da makirci da rudurwa. Saboda haka ya kai wanda ka ke so ka mori Watan Ramadan
ta ya za ka samu ganima na wannan Wata sai ka takar-kare ka dage da ayyuka. Ta
ya za ayi wannan ba tare da tsarkake dukiya ba ko wanda yake cikin tabon shan
kayan maye da aikata ashha na zunubai? Ta ya Mutum zai ji dadin karatun Al-Kur’ani
a watan Ramadan alhali bai tsarkake harshen sa daga giba ba ko kuma cin dukiyar
Jama’a ba? Annamimi, ko ta ya zai amfana da Watan Ramadan idan har yana wannan
dabi’a? Ta ya Mutumin da zuciyar sa ke cike da keta da kiyayya da hassada ga
Musulmai zai yi tsammanin amfana da wani abu na Watan Ramadan? Ta ya ya Mutum da
yake kasance tsundum cikin abinci da suturar Haramun zai samu Allah SWT ya amsa
masa addu’ar sa kamar yadda Imam Muslim ya ruwaito.
A sani Bayin Allah cewa Ubangiji Allah SWT Tsarkakakke ne
wanda bai karba face tsarkakakke, mu yi kokari wajen rabuwa da duk wani mugun
hali ko dabi’a, mu tsarkaka wajen duk abin da Allah SWT ba ya so a ko ina.
Lallai Allah SWT ya umarci masu imani da irin abin ya umarci Manzonin sa na
cewa: Ku ci daga abu mai tsarki ku kuma yi aiki na gari. Wannan kuma shi ne
umarnin da ke kan sauran masu imani. Ka da Mutum dai ya zama ya ci face daga
mai tsarki ta kowace fuska.
Allah ya ba mu fahimtar Al-Kur’ani mai girma, ya amfane
ni da ku duka daga ayoyi masu wa’azi na hikima. Allah ya tsare ni da ku daga
azabar wuta mai radadi don kuwa shi mai ji ne kuma mai gani. Allah ka dada
tsira da Annabi Muhammmad SAW da Iyalin sa ka tabbatar da yardar ka da Sahaban
sa ka kuma buwayar da Addinin Musulunci, ka rugurguza makiyan mu. Allah ka cika
ayyukan mu da abin da zai zama alheri a gare mu ka tserar da mu da kunyar
Duniya da lahira.
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga
Masallacin I.T.N-Zaria.
Twitter: @Ya_waliyyi