An fara sakin aure ta sakon WhatsApp
- Yanzu cigaba fa ya kai inda ya kai a
Duniyar sadarwa
- Wannan ya sa yanzu har aure kan
mutu ta kafafen zamani
- Mutumin ya jibgawa Matar saki bayan tayi banza da shi
Mun
samu labari cewa wani mutumi ya saki matar sa ta kafar sadarwa na zamanin nan
na WhatsApp. Cigaba dai ta kai ana sanin idan an karanta sako a WhatsApp.
Wani
Balarabe ne dai ya dankarawa Matar sa saki har 3 ta WhatsApp din a kan kurum
yayi wa matar ta sa magana amma ba ta ba sa amsa ba. Abin da ya bata masa rai
shi ne ta karanta sakon na sa amma tayi bakam ta kyale shi kamar ba ayi komai
ba.
Yanzu
cigaba ya kai inda ya kai a Duniyar sadarwa inda a kan nemi aure har ma a rabu
a kafafen zamani. Sai dai akwai ta cewa wajen sakin na sa ganin ya rubutawa
matar cewa ya sake ta har sau uku. Wasu dai na ganin cewa saki uku a lokaci
daya ya sabawa Addinin Musulunci.
Mun samu wannan labari ne daga shafin Life in
Saudi
No comments:
Post a Comment