Tuesday, August 1, 2017

Ashe barayin kasar nan su ka sa Buhari rashin lafiya?


Barayin kasar nan su ka sa Shugaba Buhari rashin lafiya

 

  • Irin satar da aka yi a Gwamnatocin baya dai ya wuce tunanin mutum
  • Sowore yace barayin kasar nan su ka sa Shugaba Buhari rashin lafiya
  • Mai Jaridar Sahara Reporters yace kudin da aka sata ya rikitar da Buhari


Omoyele Sowore yace irin mahaukaciyar satar da aka rika tafkawa a Najeriya ya sa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kwanta rashin lafiya.


Mai Jaridar nan ta Sahara Reporters Mr. Omoyele Sowore ya bayyana wannan ne a wani taro da aka yi a Landan. Sowore yace yanzu haka ma an gama sace kudin Kasar don haka babu sauran satar da ake yi.

A wani taro da aka yi a Kent a karshen makon nan Sowore yace Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya kwanta ne lokacin da ya fahimci irin satar da aka buga a Najeriya. Yanzu dai Shugaban kasar ya fara murmurewa.




Yanzu dai har Najeriya ta fita daga jerin kasashen da su ka yi kaurin suna wajen harkar cin hanci da rashawa a Duniya. Sowore yace dole Kasashen Duniya su taimaka wajen daina boye kudin sata daga Najeriya.

Wannan magana ta zo daidai da abin da wani Shehin Malami da aka yi a kasar ya fada a baya. Marigayi Albani yace idan har Buhari ya karbi mulki bakin cikin satar da aka yi kawai ya isa ya kwanar da shi kamar yadda 'Yaradua yayi fama da kudin wutar lantarki. 



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...