Monday, August 28, 2017

Hukuncin Sallar Juma'a a Ranar Idin Sallah


Ina hukuncin zuwa sallar Juma'a a ranar Sallah?


  • Mun tattaro maganar Malamai game da faduwar idi a ranar Juma'a
  • Wasu na ganin idan hakan ta faru babu wajibcin zuwa Sallar Juma'a
  • Har wasu manyan Malaman ma na ganin cewa Sallar Azahar ta fadi


A daidai lokacin da ake shirin bikin babban idi mun tattaro maganar Malamai game da faduwar idi a ranar Juma'a kamar yadda za ta kama wanna karo daga wani darasi na babban Malamin musulunci Sheikh Muhammad Sani Rijiyar Lemu.

  1. Magana ta farko
Malaman Malikiyyah sun tafi a kan cewa dole ne ayi sallar Juma'a ko da ta fadi a ranar idi don haka Allah Madaukaki yayi umarni a Qurani asali.

  1. Magana ta biyu
Malaman Shafiiyah na ganin idan hakan ta faru babu wajibcin zuwa Sallar Juma'a ga wadanda su ka fito daga kauyukan nesa amma mutanen gari za su yi Juma'a.

  1. Magana ta uku
Akwai 'yan mazhabar Hanabila da su ka tafi akan cewa idan hakan ta faru to sallar idi ta dauke Sallar Juma'a.

  1. Magana ta hudu
Akwai Malamai irin su Imam Shawkani da ke ganin idan Idi ya fado a Juma'a to har sallar Azahar ta fadi amma wannan magana na sa rauni.


Magana mafi inganci inji manyan Malamai irin su Ibn Taymiyyah ita ce za a yi sallar idi sannan kuma mustahabbi ne Liman yayi sallar Juma'a ga masu niyya amma ba dole bane don kuwa wata idin ta dauke wata. 


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...