Sunday, August 6, 2017

Ka ji abin da Ronaldo ya fadawa Alkali a gaban Kotu


Cristiano Ronaldo ya nuna cewa yana son ya dawo Ingila


  • Ana ta gabza shari'a tsakanin Cristaino Ronaldo da Hukuma
  • Dan wasan ya fadawa Alkali cewa bai aikata ba daidai ba
  • Cristiano Ronaldo yace don sunan sa ake tukhumar sa



Cristiano Ronaldo ya fusata a Kotu lokacin zaman shari'a


Ana zargin Dan wasan Duniyan nan Cristiano Ronaldo da laifin rashin biyan haraji har kudi €14.7. Dan wasan gaban na Real Madrid ya musanya zargin.

A zaman da aka yi karshe Dan wasan ya fadawa Alkali mai shari'a cewa ana kokarin a bata masa suna ne don haka aka yi masa irin wannan abu. Ronaldo yace bai taba boye dukiyar sa ya ki biyan haraji ba. Ronaldo yace dukiyar sa ba abin da za a boye bace.




Alkalin dai ya bayyana cewa babu ruwan sa da ko shi wanene illa iyaka aikin sa yake yi kamar yadda ya saba. Ronaldo yace bai taba samun irin wannan matsalar a Kasar Ingila ba don haka ne ma yake son komawa can wata rana.

Makon nan ne aka fara shiga Kotu da babban Dan wasan Real Madrid Cristaino Ronaldo inda ake zargin sa da laifin rashin biyan haraji a Kasar Sifen.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...