Saturday, August 12, 2017

Ba mamaki ASUU ta burma dogon yajin aiki


Shirin yajin aiki ya kawo dar-dar a Jami'a

  • Kungiyar ASUU na shirin shiga wani dogon yajin aiki
  • Da dama na Malaman sun zabi a tafi yajin aiki ba kakkautawa
  • Shirin yajin aiki  ya kawo dar-dar a wajen masu karatu





Mu na samun kishin-kishin din cewa Kungiyar ASUU ta Malaman Jami’a na shirin shiga wani dogon yajin aiki watakila zuwa karshen makon nan.

Kamar yadda mu ka samu labari da dama na Malaman Jami'a sun zabi a tafi yajin aikin da sai inna ta gani saboda rashin jituwa tsakanin su da Gwamnati. Shirin yajin aiki ya kawo dar-dar a wajen masu karatu a halin yanzu.

A wasu Jami'o'in irin su Usman Danfodio ta Sokoto da Ahmadu Bello ta Zariya an fara jarrabawa a halin yanzu. Wannan dai ya raba kan daliban da ke karatu. Wasu sun ce aikin yayi masu yawa dama can hutu su ke nema, wasu kuma na maza su gama.

Kungiyar ASUU ta Malaman Jami’a na ganin an ba ta hakkokin ta na albashi da sauran su da kuma kyale su cigaba da jan zaren kananan makarantun da ke karkashin Jami'a. 


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...