Wednesday, August 30, 2017

Darajar Ranar 9 ga Watan Dhul Hajj 'Arafah'


Falalar azumin Ranar Arafah a Musulunci


  • Ranar 9 ga wannan wata ce Ranar nan ta Arafah a Addinin Musulunci
  • Allah Madaukaki ya rantse da ranakun Watan da kuma ta Ranar Arafah
  • Ana karbar addua da kuma 'yanta bayin Allah a wannan Rana ta musamman




A cikin al kurani Ubangiji ya rantse da wannan rana ta Arafah da ake taruwa na musamman a Suratul Buruj.

Daga cikin darajar wannan rana akwai cewa:

  1. A wannan rana ne aka cika sakon Addinin Musulunci inda har Aya ta sauka a cikin Suratul Ma'ida
  2. Kuma a wannan rana ne ake 'yanta bayin Allah da dama kamar yadda Hadisi ya zo a littafin Sahih Muslim
  3. Har wa yau kuma babu ranar da Ubangiji yake karbar addua kamar wannan rana wanda shi ma ya zo a littafin Silsilal hadith na Sheikh Nasir Deen Albany.
Duk wani Mahajjaci a wannan rana ya dukafa ana kuma neman rahamar Allah. Ana son azumi ga wadanda ba su je Hajji ba wanda ke kankare zunuban shekara biyu. Azumin ranar Arafah na yafe zunuban shekarar bara da kuma shekarar bana da ake ciki inji Manzon Allah SAW.


Dr. Isa Ibrahim Ali Pantami yayi wannan jawabi a wani karatu da yayi

Monday, August 28, 2017

Hukuncin Sallar Juma'a a Ranar Idin Sallah


Ina hukuncin zuwa sallar Juma'a a ranar Sallah?


  • Mun tattaro maganar Malamai game da faduwar idi a ranar Juma'a
  • Wasu na ganin idan hakan ta faru babu wajibcin zuwa Sallar Juma'a
  • Har wasu manyan Malaman ma na ganin cewa Sallar Azahar ta fadi


A daidai lokacin da ake shirin bikin babban idi mun tattaro maganar Malamai game da faduwar idi a ranar Juma'a kamar yadda za ta kama wanna karo daga wani darasi na babban Malamin musulunci Sheikh Muhammad Sani Rijiyar Lemu.

  1. Magana ta farko
Malaman Malikiyyah sun tafi a kan cewa dole ne ayi sallar Juma'a ko da ta fadi a ranar idi don haka Allah Madaukaki yayi umarni a Qurani asali.

  1. Magana ta biyu
Malaman Shafiiyah na ganin idan hakan ta faru babu wajibcin zuwa Sallar Juma'a ga wadanda su ka fito daga kauyukan nesa amma mutanen gari za su yi Juma'a.

  1. Magana ta uku
Akwai 'yan mazhabar Hanabila da su ka tafi akan cewa idan hakan ta faru to sallar idi ta dauke Sallar Juma'a.

  1. Magana ta hudu
Akwai Malamai irin su Imam Shawkani da ke ganin idan Idi ya fado a Juma'a to har sallar Azahar ta fadi amma wannan magana na sa rauni.


Magana mafi inganci inji manyan Malamai irin su Ibn Taymiyyah ita ce za a yi sallar idi sannan kuma mustahabbi ne Liman yayi sallar Juma'a ga masu niyya amma ba dole bane don kuwa wata idin ta dauke wata. 


[NAIJ Hausa]

Thursday, August 24, 2017

Dan wasa Cristiano Ronaldo ne gwarzon UEFA na 2017

UEFA ta zabi Ronaldo a matsayin babban Dan wasan Turai

 

  • Dan wasan Real Madrid Cristiano Ronaldo ne gwarzon UEFA a bana
  • Yanzu nan UEFA ta zabi Ronaldo a matsayin babban Dan wasan Turai
  • Sauran 'Yan Real Madrid din sun ciri tuta a wajen fitar da gwani da ake yi


 Labari ya iso mana yanzu nan cewa UEFA ta zabi Cristiano Ronaldo a matsayin babban Dan wasan Turai na shekarar nan.

Babban Dan wasan na Real Madrid Cristiano Ronaldo ne gwarzon UEFA mai kula da kwallon kafan Turai a shekarar nan ta bana. Dan wasan ne kuma aka zaba gwarzon Dan wasan gaba na wannan shekarar. Fitaccen Dan kwallon Ronaldo dai ya tashi da kyaututtuka yau dinnan.

Har wa yau sauran 'Yan wasan Real Madrid din irin su Sergio Ramos sun ciri tuta. An zabi Ramos a matsayin Dan bayan da tauraruwar sa ta ke haskawa bana. An kuma zabi Luka Modric a matsayin gwarzon Dan wasan tsakiya na shekarar nan ta 2016.

Dan wasan gaban na Real Madrid ya lashe Gasar UEFA Champions league da UEFA SuperCup na bana da bara da Kungiyar sa ta Real Madrid ya kuma jefa kwallayen da su ka fi na kowa.



[NAIJ Hausa]

Wani mutumi ya tikawa Matar sa saki ta WhatsApp


An fara sakin aure ta sakon WhatsApp  


  • Yanzu cigaba fa ya kai inda ya kai a Duniyar sadarwa
  • Wannan ya sa yanzu har aure kan mutu ta kafafen zamani
  • Mutumin ya jibgawa Matar saki bayan tayi banza da shi





Mun samu labari cewa wani mutumi ya saki matar sa ta kafar sadarwa na zamanin nan na WhatsApp. Cigaba dai ta kai ana sanin idan an karanta sako a WhatsApp.

Wani Balarabe ne dai ya dankarawa Matar sa saki har 3 ta WhatsApp din a kan kurum yayi wa matar ta sa magana amma ba ta ba sa amsa ba. Abin da ya bata masa rai shi ne ta karanta sakon na sa amma tayi bakam ta kyale shi kamar ba ayi komai ba.

Yanzu cigaba ya kai inda ya kai a Duniyar sadarwa inda a kan nemi aure har ma a rabu a kafafen zamani. Sai dai akwai ta cewa wajen sakin na sa ganin ya rubutawa matar cewa ya sake ta har sau uku. Wasu dai na ganin cewa saki uku a lokaci daya ya sabawa Addinin Musulunci.


Mun samu wannan labari ne daga shafin Life in Saudi

Wednesday, August 23, 2017

Dan kwallon Ingila Rooney yayi ritaya


Babban Dan wasan Ingila ya ajiye kwallo a gida

  • Wayne Rooney yayi sallama da takawa kasar sa leda
  • Dan kwallon yace lokacin yayi da zai bar wa yara fage
  • Kyaftin din Ingila mai shekaru 31 da ya ajiye kambu

Dan wasan gaban nan Wayne Rooney yayi sallama da takawa kasar sa leda dazu nan. Dan wasa Rooney yayi ritaya yana shekara 31.

Babban Dan kwallon yace lokaci yayi da zai bar wa yara fage bayan yayi shekara 14 yana bugawa Kasar Ingila wasa. Kyaftin din na Ingila mai shekaru 31 dai ya ajiye kambu bayan tattaunawa da Kocin kasar Ingilar da kuma Kocin Kungiyar Everton.

A kakar bana ne dai tsohon Dan wasan nan Manchester United ya koma Kungiyar sa ta gida watau Everton inda yanzu har ya jefa kwallaye biyu. Dan wasan yace ba abu ne mai sauki barin Kulob din ba kuma yanzu ya ajiye kwallo a Kasar sa don ya maida hankali da kyau.



[NAIJ Hausa]

Wednesday, August 16, 2017

UEFA ta fito da gwarzon 'Yan kwallon shekarar nan


Manyan ‘Yan kwallo 3 da za a zaba zakaran Turai


An kawo Ronaldo cikin manyan 'Yan wasan Turai

Haka kuma an sa takwaran sa Lionel Messi na Barcelona

Na karshen su shine Dan wasa mai tsaron raga Buffon




A jiya UEFA ta fito da gwarzon 'Yan kwallon shekarar nan guda 3 wanda a cikin su ne za a fitar da gwani na gwanaye. Kun dai ji 'Yan kwallon su ne:

  1. Cristiano Ronaldo
Dan wasan gaban na Real Madrid ya lashe Gasar bana na UEFA Champions league da Kungiyar sa ta Real Madrid ya kuma jefa kwallaye a wasanni karshe da na kusa da karshen da su ka kawo nasara.

  1. Lionel Messi
Duk da Dan wasan bai isa zagayen karshe na Gasar UEFA Champions league ba amma yana cikin wadanda su ka yi zarra kamar kowace kaka a Turai. Messi ya jefa kwallaye rututu a Gasar bara.

  1. Gianligui Buffon
Dan wasan da ke tsaron ragar Juventus ya samu shiga bayan irin kokarin da ya tabuka a bara. Kafin wasan karshe dai kwallaye kadan aka iya zurawa Buffon a ragar sa.



[NAIJ Hausa]

Tuesday, August 15, 2017

Wasu kalmomin da Turawa su ka aro daga Yaren Najeriya


Ashe Bature ya kan aro kalma daga Hausa ko Ibo?

  •  Akwai wasu kalmomin da Turawa su ka aro daga Najeriya
  • Turawa sun ari wasu kalmomi daga Ibo da Hausa da Efik
  • Daga cikin wadannan kalmomi dai akwai irin su Juju da sauran su


Kamar kwanakin baya wannan karo mun kawo maku jerin wasu kalmomi da aka aro daga harsunan Najeriya zuwa Ingilishi. Kadan daga ciki:

  1. Okra
Asali wannan kalma ta Okra gggdaga harshen Ibo aka dauko ta. Turawa na kiran kubewa da Okra a Ingilishi.

  1. Bogus
Asali wannan kalma daga Hausa ta fito kamar yadda masana su ka fada. Yanzu Bature kan yi amfani da wannan kalma.

  1. Juju
Asali ma dai Juju kalmar daga Najeriya aka dauko ta. Juju na nufin abin da ya shafi Aljanu ko kuma wata rawa ta mutanen mu.

  1. Tango
Haka dai kalmar Tango asali daga harshen Ibibio na mutanen Kasar Kudu ta fito wanda ainihi rawa ne na mutanen Yankin.

  1. Buckra

A yaren mutanen Efik, Buckra na nufin Bawa wanda Turawa su ka ara su ke kiran bakin mutum ko kuma Talaka farin fata.

  

Sunday, August 13, 2017

Kalmomi 5 da Hausawa su ka aro daga Larabawa



Kalmomin Larabci da aka aro a harshen Hausa


  • Hausawa sun ari wasu kalmomi daga harshen Larabci
  • Daga cikin irin wannan kalmomi akwai sukari da Aljani
  • Ko me ya hada Malam Bahaushe haka da Balarabe?





Ba shakka Malam Bahaushe ya ari wasu kalmomin sa daga harshen Larabci. Da yawa dai daga ji za ka fahimci daga inda aka kalo su. Ga dai wasu 5 nan daga ciki yau da mu ka kawo:

  1. Sukari
Da Larabci ana cewa As-sukar wanda kuma shi ne Bature ya ke kira Sugar. Ko daga wajen wa aka fara aro kalmar?

  1. Kofi
Bature ma dai ya kan kira Kofi da suna CUP watau abin da Balarabe yake kira KAUB. Ka kuma dai ji wani sabo!

  1. Al-Jinn
Shi Bahaushe kamar Balarabe ya san da Aljannu abin da Larabawa ke kira Al-jinn. Turawa ma dai yana su kan kira su Jinns da Ingilishi.

  1. Albasa
Kusan a yare da dama Albasa ba ta canza suna ba a Najeriya. Haka dama aka san wannan suna wajen Balarabe watau Al-baslun.

  1. Sabulu

Sabulu ma dai da Larabci asalin sunan sa Sabun. Bayan wannan dai akwai aron kalmomi da dama tsakanin Hausa sa Larabci. 


[NAIJ Hausa]

Saturday, August 12, 2017

Ba mamaki ASUU ta burma dogon yajin aiki


Shirin yajin aiki ya kawo dar-dar a Jami'a

  • Kungiyar ASUU na shirin shiga wani dogon yajin aiki
  • Da dama na Malaman sun zabi a tafi yajin aiki ba kakkautawa
  • Shirin yajin aiki  ya kawo dar-dar a wajen masu karatu





Mu na samun kishin-kishin din cewa Kungiyar ASUU ta Malaman Jami’a na shirin shiga wani dogon yajin aiki watakila zuwa karshen makon nan.

Kamar yadda mu ka samu labari da dama na Malaman Jami'a sun zabi a tafi yajin aikin da sai inna ta gani saboda rashin jituwa tsakanin su da Gwamnati. Shirin yajin aiki ya kawo dar-dar a wajen masu karatu a halin yanzu.

A wasu Jami'o'in irin su Usman Danfodio ta Sokoto da Ahmadu Bello ta Zariya an fara jarrabawa a halin yanzu. Wannan dai ya raba kan daliban da ke karatu. Wasu sun ce aikin yayi masu yawa dama can hutu su ke nema, wasu kuma na maza su gama.

Kungiyar ASUU ta Malaman Jami’a na ganin an ba ta hakkokin ta na albashi da sauran su da kuma kyale su cigaba da jan zaren kananan makarantun da ke karkashin Jami'a. 


[NAIJ Hausa]

Friday, August 11, 2017

An sa mata suna 'Kuri'a' bayan an haife ta a layin zabe



An radawa wata yarinya suna 'Kuri'a' bayan an haife ta a layin zabe 

  • An haifi wata yarinya yayin da ake shirin kada kuri'a
  • Wannan abu ya faru ne a can kasar Kenya
  • An radawa wanan yarinya da aka haifa suna 'Kura'





A can kasar Kenya da ake shirin zabe an haifi wata yarinya bayan wata mata ta buge da nakuta ana shirin kada kuri'a.

Wata mata mai suna Pauline Chemanang ta buge da nakuda yayin da ake kokarin zabe a Kasar Kenya. Nan take wannan mata ta haifi diya mace a filin kada kuri'a da ke wata Makarantar Sakandare mai suna Konyaq a Yammacin Garin Pokot.


Madam Paulina Chemanang ta sauka lafiya bayan nan kuma ta dawo domin kada kuri'ar ta. Ko da aka tambayi sunan diya sai tace sunan yarinya 'kura' Chepkura. A yaren kasar Kenya na Swahili ma'anar sunan shi ne kuri'a ko kuma ka ce 'zabe'. 




[NAIJ Hausa]

Za a hau yanar gizo kyauta yau a Najeriya


Albishirin ku: Masu layin GLO za su ci bagas


 
  • Globacom za su bada goron Juma'a a Yau
  • Masu layin za su hau yanar gizo a kyauta
  • Sai dai akwai wasu sharuda kafin a dace



Labari ya zo mana cewa masu layin Glo za su gwangwaje kyauta yau a Najeriya muddin sun sa katin waya ciki 'yan kwanakin nan.

Kamfanin sadarwa na Globacom na kasar za su bada goron Juma'a  wanda shi ne karo na farko a Kasar domin a hau shafin gizo kyauta ba tare da ko sisi ba. Za dai a bada kyautar mega byte 200 domin a yi abin da aka ga dama.

Kenan dai masu layin za su hau yanar gizo a kyauta goben. Sai dai akwai wasu sharuda kafin a dace da wannan wanda shine mutum ya zama yayi amfani da katin waya na N250 ko kuma ya kashe mega byte na hawa yanar gizo 100 da kuma N150.

Kwanaki dai Hukumar NCC da ke kula da harkokin sadarwa na zamani tayi kira ga jama'a da su saurari sabon farashin hawa shafin Internet. Mun kuma ji kishin-kishin din ana kokari a dakatar da wannan bagas da GLO za ta bada.



[NAIJ Hausa]

Thursday, August 10, 2017

Ka taba jin abin da kowane Dan Majalisa yake samu a wata?


Kowane Dan Majalisar Najeriya ya karbi albashin sama da Miliyan 200


  • 'Yan Majalisar sun karbi albashin sama da Miliyan 200
  • A kowace wata dai su kan tashi da Naira Miliyan 10
  • 'Yan Majalisar kasar dai sun ci fiye da rabin wa'adin su


Kamar yadda ku ka ji 'Yan Majalisar Najeriya sun karbi albashin sama da Miliyan 200 cikin shekaru biyun da su ka wuce zuwa yau.

Lissafi ya nuna cewa kusan watanni 22 ne dai kacal su ka ragewa 'Yan Majalisar kasar su sauka daga mulki. Kowane Dan Majalisar ya kan samu kudin aiki na kusan Naira Miliyan 8 sannan kuma ga wasu 'yan kari na kusan Miliyan guda a wata.

Tun da a wata kowane na tashi da sama da Miliyan 8 kenan cikin fiye da shekaru biyu kowa ya karbi akalla Naira Miliyan 214. An dai kashe fiye da Naira Biliyan 32 wajen albashin 'Yan Majalisan Kasar daga 2015 zuwa yanzu.

Jaridar Daily Trust tayi wannan nazari inda tace dai kusan kusan rabin 'Yan Majalisa ne su ka gabatar da kudiri tun hawan su Gwamnati yayin da sauran 'Yan Majalisa musamma na Arewa fiye da 160 kenan dai ba su gabatar da wani kudiri ba.


[NAIJ Hausa]


Tuesday, August 8, 2017

Real Madrid za ta goge raini da Manchester United


Gasar UEFA Super Cup: Man United za ta gwabza da Real Madrid

 


Kungiyar Manchester United za ta gwabza da Real Madrid

Za a kara ne a wasan cin kofin UEFA Super Cup a daren yau

Dan wasa Cristiano Ronaldo zai hadu da tsohon Kulob din sa




A daren yau Manchester United za ta gwabza da Real Madrid a filin Philip II Arena da ke Skopje a Kasar Macedonia.

Za a kara ne a kofin UEFA Super na Zakarun Turai wadanda su ka kashe kofin Champions League da Europa League a kakar bara. A cikin kwanakin nan Real Madrid ta buga da Manchester United inda kamar sauran wasannin ta ta sha kashi.

Sai dai a yau Talata manyan 'Yan wasan Real Madrid din za su dawo. Babban Dan wasa Madrid kuma tsohon Dan wasan Man Utd Cristiano Ronaldo zai buga wasan. Haka kuma kyaftin din Real Madrid Sergio Ramos. Madrid ta lashe kafin a bara.

Ba shakka dai Kocin Manchester Jose Mourinho ya san irin illar da Real Madrid za ta iya amma dai shi ma ya kawo sababbin 'Yan wasa irin su Romelu Lukaku. Haduwar Kungiyar na karshe dai Real Madrid din Mourinho tayi nasara kan Koci Ferguson lokacin yana United.



[NAIJ Hausa]

Monday, August 7, 2017

Shin ka san irin amfanin filanten a jikin mutum


Ko ka san cewa filanten na da matukar amfani?


  • Bincike ya nuna cewa filanten da amfani kwarai da gaske

  • Filanten na dauka da bitamin da sauran sinadarai iri-iri

  • Filanten na maganin hawan jini da kuma rage nauyi






  1. Hawan jini
Yawan cin filanten na sa jinin mutum ya tsaya daidai ba tare da hawa sama ko sauka kasa ba saboda irin sinadarai na fotash.


  1. Nauyi
Filanten na kokari wajen tsagaita nauyin mutum ya zama bai zama rusheshe ba. Filanten na kula da yawan sukarin da ke jikin mutum.


  1. Maganin cutar sukari
Haka kuma filanten na yakar cutar nan na sukari watau dayabatis. Sinadarin magnesium na kula da yanayin sikarin da ke jikin mutum.


  1. Gyara kwakwalwa
Masana sun ce filanten na dauke da kaso da dama na Bitamin B6 wanda ke gyara kwakwalwa wasai. Filanten na kuma rage ciwon kai.


  1. Kwarin kashi
Filanten na dauke da Sinadarin kashium da ke kara kwarin kashi da jijiyoyi da na na hakori da akaifu a jikin mutum.




Mun dauko wannan daga Jaridar Thecablestyle


Sunday, August 6, 2017

Ka ji abin da Ronaldo ya fadawa Alkali a gaban Kotu


Cristiano Ronaldo ya nuna cewa yana son ya dawo Ingila


  • Ana ta gabza shari'a tsakanin Cristaino Ronaldo da Hukuma
  • Dan wasan ya fadawa Alkali cewa bai aikata ba daidai ba
  • Cristiano Ronaldo yace don sunan sa ake tukhumar sa



Cristiano Ronaldo ya fusata a Kotu lokacin zaman shari'a


Ana zargin Dan wasan Duniyan nan Cristiano Ronaldo da laifin rashin biyan haraji har kudi €14.7. Dan wasan gaban na Real Madrid ya musanya zargin.

A zaman da aka yi karshe Dan wasan ya fadawa Alkali mai shari'a cewa ana kokarin a bata masa suna ne don haka aka yi masa irin wannan abu. Ronaldo yace bai taba boye dukiyar sa ya ki biyan haraji ba. Ronaldo yace dukiyar sa ba abin da za a boye bace.




Alkalin dai ya bayyana cewa babu ruwan sa da ko shi wanene illa iyaka aikin sa yake yi kamar yadda ya saba. Ronaldo yace bai taba samun irin wannan matsalar a Kasar Ingila ba don haka ne ma yake son komawa can wata rana.

Makon nan ne aka fara shiga Kotu da babban Dan wasan Real Madrid Cristaino Ronaldo inda ake zargin sa da laifin rashin biyan haraji a Kasar Sifen.


[NAIJ Hausa]

Friday, August 4, 2017

Na ji dadin yadda na ga Buhari Inji Babban Limamin Landan



Babban Faston Ingila ya ziyarci Buhari yace ya ga ikon Allah


 -          Babban Limamin Landan ya kai wa Shugaba Buhari ziyara


-          Faston yace ya ji dadin yadda ya ga Muhammadu Buhari


-          Justin Welby yace warakar da Shugaban ya samu ikon Allah ne




Mai magana da yawun-bakin Shugaban kasar Najeriya watau Femi Adesina ya bayyana cewa dazu Shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi wani babban bako.

Babban Faston Kasar Birtaniya Archbishop na Canterbury Justin Welby wanda Aminin Shugaban kasar ne ya taka domin ziyarar Shugaba Buhari. Ba wannan bane karon farko da Limamin ya ziyarci Shugaba Buhari a Landan.

Faston yayi murna da yadda ya ga Shugaban kasar. Welby yace Shugaba Buhari yana samun sauki matuka don tuni har ya murmure sosai. Babban Limamin yace wannan duk ikon Ubangiji ne don shi ke ba da lafiya da waraka.

Dazu mu ka ji cewa Limamin Kalaba za su cigaba da yi wa Shugaba Muhammadu Buhari addua. Shugaban kasa Muhammadu Buhari na ta faman jinya a Landan ya kuma ji dadin wannan Fasto Aminin sa.  


[NAIJ Hausa]

Thursday, August 3, 2017

Neymar zai rika karbar Naira Miliyan 36 kullum a PSG

Neymar zai rika karbar albashin Biliyoyi a shekara


 


Yanzu Dan wasa Neymar zai rika karbar albashin Biliyoyi a shekara

A kowace rana ta Allah zai tashi da sama da Naira Miliyan 30

A kowace awa guda Dan wasan zai samu sama da Miliyan guda





Ko barci Neymar yayi ya tashi a rana ba mamaki zuwa wannan lokaci ya hada kusan Naira Miliyan 10 a sabon Kulob din da ya koma PSG.

Dan wasan da a cikin talauci ya tashi ya amince da yarjejeniyar shekaru biyar inda za a kashe kudi har sama da Dala Miliyan 500. A kowace rana ta Allah Neymar zai tashi da akalla Naira Miliyan 36.

Da mu kayi lissafi dai mun fahimci cewa Dan wasa Neymar zai rika karbar albashin sama da Naira Biliyan uku a shekara. A kowace awa guda Dan wasan zai samu sama da Miliyan guda na Naira.

Dama dai kun ji cewa Idan komai ya yiwu Kungiyar Barcelona za ta saida Tauraron Dan wasan ta Neymar zuwa Kungiyar PSG na Faransa kan kudin da zai girgiza Duniya.



[NAIJ HAUSA]

Wednesday, August 2, 2017

Babban Dan wasan Barcelona yayi sallama da Kulob din



Neymar zai zama Dan wasan da ya fi kowa tsada a Duniya?


 

  • Barcelona za ta saida Tauraron Dan wasan ta Neymar
  • Kungiyar ta ba Neymar Jr. Izini ya tattauna da PSG
  • Dan wasan zai zama mafi tsada a Duniya idan ta tabbata


Idan komai ya yiwu Kungiyar Barcelona za ta saida Tauraron Dan wasan ta Neymar zuwa Kungiyar PSG na Faransa kan kudin da zai girgiza Duniya.

Barcelona ta ba Dan wasan na ta izinin ganawa da PSG dazu. Barcelona ta sha alwashin karbar kudi har Dalar Euro Miliyan €222. Kungiyar ta Barcelona tace dole sai an biya wannan makudan kudi a nan take watau a zuwa daya.

Tuni dai Dan wasan da Dillalin sa Mahaifin sa ya fadawa abokan sa cewa ya tafi kenan. Dan wasan yayi ban kwana da abokan sa da sauran 'Yan kulob cewa zai koma Birnin Faris. Wannan dai zama ciniki mafi tsada a Duniyar kwallon kafa.



[NAIJ Hausa]


Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...