Wednesday, May 10, 2017

Ka taba ganin matan Gwamnonin Arewa


Uwargidan Gwamnonin Arewa da inda su ka yi karatu [Cikin Hotuna]



– Mafi yawan Gwamnonin Arewa su na da ofisihin Uwargida na iyalan su


– Sai dai wasu Gwamnonin ba su jefa matan su cikin harkar shugabanci ba


– Ga dai kadan daga cikin matan Gwamnonin Arewa maso yamma



Mun kawo maku hotunan matan Gwamnonin Arewa. Irin su Gwamna Ibrahim Geidam dai ba a san matar sa ba. Don wasu Gwamnonin ba su bari matan su su shiga cikin sha’anin mulki


1.      Matar Gwamnan Jihar Adamawa: Hajiya Maryam Muhammad Umar Jibrilla



Matar Gwamnan Jihar Adamawa ‘yar gidan Sani Zangon-Daura ce wanda fitacce ne a Katsina da Najeriya. Tayi karatu har Digir-gir a Kasar Birtaniya.



2.      Matar Gwamnan Jihar Bauchi: Hajiya Hadiza Mohammed Abubakar


Abin da zai burge ka shi ne tun shekarar 1979 ta auri Mijin ta wanda yanzu ya zama Gwamna. Tayi Digiri har 2 a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya.



3.      Matar Gwamnan Jihar Borno: Hajia Nana Kashim Shettima


Ana mata lakabi da Uwar Marayu ita ma tayi karatu a Jami’ar Maiduguri kamar dai Mijin ta Kashim Shettima.


4.      Matar Gwamnan Jihar Gombe: Hajia Adama Dankwambo



Uwargidar Mai girma Gwamna Dankwambo na Jihar Gombe kuma tana bakin kokari wajen dafawa Mijin ta.




[NAIJ.com]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...