Wednesday, May 24, 2017

Ahmed Musa ya auri Juliet bayan ya rabu da Jamila


Karamar magana ta zama babba: Ahmed Musa ya angonce da Juliet Ejue


 – Babban Dan wasan Super Eagles Ahmed Musa ya auri Juliet


– Dan wasan na Najeriya ya saki matar sa kwanaki


– An ji cewa matar tace sam ba za ta zauna da kishiya ba




Da alama Ahmed Musa ya auri sahibar sa Juliet. Dan wasan mai shekaru 24 ya shiga daga ciki. Kwanaki dai ya rabu da matar sa Jamila.

Ko ka dai har yanzu ba mu samu tabbaci ba amma ba mamaki babban dan wasan gaban Super Eagles Ahmed Musa ya auri Sahibar sa Juliet Ejue. Mun dai ga wasu hotuna da takwarar sa 'dan wasan Najeriya Juwon Oshinawa ya dora na yawo da ke nuna hakan.

Kwanaki dai Ahmed Musa ya rabu da uwar ‘ya ‘yan sa bayan yayi niyyar kara mata inda ta tubure tace ba za ta sabu ba. Mun ji cewa dai sun rabu bayan ya ba ta kyautar wata katuwar mota da gida a Kano.

Tun a Kano dai Ahmed Musa ya hadu da Jamila sai dai yanzu ya zama Angon Juliet wata mutumiyar Garin Kalaba na Jihar Kuros-Riba. Musa dai ya sayawa Juliet gida a Lekki da ke Legas da kuma zugegiyar Marsandi.



[NAIJ Hausa] 

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...