Sunday, May 14, 2017

Ebola ta dawo Nahiyar Afrika



La haula: Cutar Ebola ta dawo Afrika


 – Cutar nan Ebola ta dawo cikin Nahiyar Afrika


– Yanzu haka cutar ta kashe Jama’a a kasar Congo


– Ebola dai tana kisa cikin lokacin kan-kani



Cutar nan da ta kashe Jama’a ta kara dawowa Afrika. Dama kwanakin bayan WHO tace babu makawa sai cutar Ebola ta dawo. Dole Jama’a su yi hattara domin cutar na kisa.

Tun a kwanakin baya muka bayyana maku cewa Cutar nan ta Ebola na shirin dawawo kasashen Duniya. Sai dai ba a san a ina cutar za ta barke ba kamar yadda Hukumar kula da lafiya ta Duniya WHO ta fada.

Sai dai ga shi yanzu cutar ta barke a Kasar Congo inda har mutane akalla 3 sun bakunci lahira. Ministan lafiya na kasar ya tabbatar da wannan bayan an samu Jama’a da dama na fama da zazzabi.

Shekaru 3 da su ka wuce cutar ta hallaka mutane kusan 50 a annobar da ta barke. Gaba daya dai a shekarar 2013 annobar tayi barna a Afrika musamman irin su kasar Liberia, Guinea, da Sierra Leone inda aka rasa mutane sama da 11,000.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...