Wednesday, May 31, 2017

Turnuku fadan aljanu: Sojoji sun kashe Jami'an 'Yan Sanda


Rikicin ‘Yan Sanda da Sojoji bai yi dadi ba a Kalaba






Yadda rikicin Sojoji da ‘Yan Sanda ya ga bayan Jami’ai da dama



 – Sojojin Najeriya sun kai wa ‘Yan Sanda hari a Garin Kalaba


– Ba mamaki wasu manyan Jami’an ‘Yan Sanda sun rasa ran su


– Abin ya kai har an kona ofishin ‘Yan Sanda



  • Rikicin Sojoji da ‘Yan Sanda ya bar gawawwaki Jami’ai da dama
  • An yi fada ne tsakanin ‘Yan Sanda da Sojojin ruwa
  • Daga baya dai Sojojin sama da kasa su ka shigo ciki


Mun samu labari daga kafafe da dama cewa jiya da dare an yi wani mugun fada tsakanin ‘Yan Sanda da Jami’an Sojoji wanda yayi sanadiyar mutuwar ‘Yan Sanda da dama. Majiyar mu tace an fara rikicin ne da Sojojin ruwa daga baya sauran Sojoji su ka kutso ciki.

Wanda ya ji yadda abin ya faru cikin dare ya bayyana mana cewa an kona ofishin ‘Yan Sanda. Abin dai ya kai an bude barikin Sojoji kowa ya dauki manyan makamai inda aka shiga budawa ‘Yan Sandan wuta. An dai ce an harbi wani Sojan ruwa ne a hannu.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...