Wednesday, May 10, 2017

UCL: Kungiyar Juventus ta kai wasan karshe


Champions League: Juventus ta karasa zagayen karshe


 – Kungiyar Juventus ta karasa zagayen karshe a gasar Uefa Champions League


– Sau 2 kenan cikin shekaru 3 Juventus din tana kai wannan matsayi


– Ko wannan karo za a dace a Birnin Cardiff?





Monaco ta kara shan kashi a hannun Juventus a Gasar zakarun Nahiyar Turai. Dani Alves ya nuna cewa har yanzu akwai sauran ta a kafar sa a wasan. Matashin Dan wasa Mpape ya zurawa Buffon kwallo a raga.

Kungiyar Juventus ta kasar Italiya ta isa zagayen karshe a gasar UEFA Champions League na zakarun Nahiyar Turai bayan ta doke Monaco ta Faransa da ci 2-1. A zagayen farko Juventus tayi nasara da ci biyu da nema.




Dan wasa Madzukic da Dani Alves ne su ka fatattaki Monaco yayin da Dan wasan ta Mpape ya zama mai mafi karancin shekarun da ya taba cin kwallo a wannan zagaye na Gasar. Juventus za ta kara karawa a wasan karshe da Kulob din Madrid a Birnin Cardiff.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...