Damukaradiyya
a Najeriya: Hanyar da aka baro da inda aka kamo!
– Damukaradiyyar Najeriya ta balaga a halin yanzu
– Sau biyu Soji na yin katsalandan a harkar siyasa
– Tun daga 1999 farar hula ke mulkin kasar nan
Muhammad Malumfashi ya rubuta wannan a yau da ake bikin murnar Damukaradiyya a Najeriya.
- Yanzu dai ba shakka Damukaradiyya tayi karfi a Najeriya
- A baya dai sau biyu Sojoji na kifar da Gwamnatin farar hula
- An yi haka a shekarar 1966 da kuma 1983
Ka iya cewa Damukaradiyyar
Najeriya ta balaga bayan an yi shekaru 18 ana bugawa babu tangarda. Ana kuma sa
ran cewa abubuwa ma sai dai kyau kurum za su kara duk da cewa an fara jin
kishin-kishin din juyin mulki, sai dai kamar 2010, babu inda yunkurin zai kai.
A rana irin ta yau Janar
Abdussalami Abubakar ya mikawa tsohon shugaba a mulkin Soja Janar Olusegun
Obasanjo mulki. Har yau kuma tana hannun farar hula inda mutanen kudu su kayi
kusan shekaru 14 inda ‘Yan Arewa su ka yi mulkin shekaru 4.
Akwai maganar cewa Shugaba
Obasanjo ya nemi ya zarce fiye da wa’adin sa, uwar-bari dai ta sa dole ya
kakaba tsofaffin Gwamnoni Marigayi Ummaru ‘Yaradua da Goodluck Jonathan. Bayan
rashin lafiya ta kashe Ummaru ‘Yaradua ne Jonathan ya dare mulkin kasar har ya
zarce.
An samu hadakar Jami’iyyun
adawa inda su ka yi kutun-kutun su ka tika Shugaba Jonathan da kasa. Jam’iyyar
APC ta su wani Janar din, Muhammadu Buhari ta karbi mulki wanda kawo yanzu shugaban kasar da wasu
tulin alkawuran da APC ta dauka na kwance. Tuni dai har wasu sun fara hangen
2019!
No comments:
Post a Comment