Monday, May 29, 2017

Ranar bikin murnar Damukaradiyya a Najeriya



Damukaradiyya a Najeriya: Hanyar da aka baro da inda aka kamo!



Damukaradiyyar Najeriya ta balaga a halin yanzu


– Sau biyu Soji na yin katsalandan a harkar siyasa


Tun daga 1999 farar hula ke mulkin kasar nan





Muhammad Malumfashi ya rubuta wannan  a yau da ake bikin murnar Damukaradiyya a Najeriya.


  • Yanzu dai ba shakka Damukaradiyya tayi karfi a Najeriya
  • A baya dai sau biyu Sojoji na kifar da Gwamnatin farar hula
  • An yi haka a shekarar 1966 da kuma 1983


Ka iya cewa Damukaradiyyar Najeriya ta balaga bayan an yi shekaru 18 ana bugawa babu tangarda. Ana kuma sa ran cewa abubuwa ma sai dai kyau kurum za su kara duk da cewa an fara jin kishin-kishin din juyin mulki, sai dai kamar 2010, babu inda yunkurin zai kai.

A rana irin ta yau Janar Abdussalami Abubakar ya mikawa tsohon shugaba a mulkin Soja Janar Olusegun Obasanjo mulki. Har yau kuma tana hannun farar hula inda mutanen kudu su kayi kusan shekaru 14 inda ‘Yan Arewa su ka yi mulkin shekaru 4.




Akwai maganar cewa Shugaba Obasanjo ya nemi ya zarce fiye da wa’adin sa, uwar-bari dai ta sa dole ya kakaba tsofaffin Gwamnoni Marigayi Ummaru ‘Yaradua da Goodluck Jonathan. Bayan rashin lafiya ta kashe Ummaru ‘Yaradua ne Jonathan ya dare mulkin kasar har ya zarce.

An samu hadakar Jami’iyyun adawa inda su ka yi kutun-kutun su ka tika Shugaba Jonathan da kasa. Jam’iyyar APC ta su wani Janar din, Muhammadu Buhari ta karbi mulki wanda kawo yanzu shugaban kasar da wasu tulin alkawuran da APC ta dauka na kwance. Tuni dai har wasu sun fara hangen 2019!



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...