Wednesday, May 31, 2017

An sace wani Dan Majalisar Tarayya


An sace wani Dan Majalisa a hanyar Kaduna-Abuja 



 Masu garkuwa da mutane sun yi gaba da wani Dan Majalisar Tarayya


– Yanzu haka an nemi Dan Majalisar Sumaila da Takai an rasa


– Honarabul Durbunde ya fada hannun barayi






  • Masu garkuwa da mutane sun sace wani Dan Majalisa
  • Yanzu haka mu ke samun wannan labari
  • An dai nemi Dan Majalisar Jihar Kano ba a san inda yayi ba

Ba mamaki masu garkuwa da mutane sun yi gaba da wani Dan Majalisar Jihar Kano mai wakiltar Yankin Sumaila da Takai a Majalisar Tarayya. Yanzu haka dai NAIJ.com ke samun wannan labari maras dadi.

Ana dai samun karuwar masu garkuwa da mutane a Najeriya tun ba yau ba. Yanzu haka dai an nemi Honarabul Garba Durbunde an rasa yayin da yake hanyar komawa gida Kano daga Birnin Tarayya Abuja a daidai hanyar Jere jiya.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...