Tuesday, May 23, 2017

Bam ya kashe mutane sama da 22 a Manchester


 
Shugabannin kasashe sun yi tir da harin da aka kai a kasar Birtaniya



– Shugabannin kasashe sun yi tir da harin da aka kai a kasar Birtaniya


– ‘Yan ta’adda sun kai wani mugun hari inda aka kashe Jama’a da dama


– Har yanzu dai ana zaman dar-dar a Garin Manchester




Wani ‘Dan ta’adda ya kai wani mugun hari a Garin Manchester na Ingila inda fiye da mutane 20 su ka mutu nan take. Mutane akalla 60 kuma sun jikkata a harin.

Wani Dan ta’adda ya kashe mutane 22 a wani hari da ya kai a Garin Manchester yayin da wasu da dama su ka samu rauni. Shugabannin kasashen Duniya irin su India, Japan, Canada, da Australlia dai sun yi tir da wannan mugun hari.

Shugabannin Jam’iyyu dai sun daga kamfen din zabe a dalilin hakan. Kungiyar ISIS ta Duniya dai ta fitar da sakonni inda ta ke murnar harin da aka kai. Abin dai ya faru ne ana wani shirin wasa na waka.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...