Sunday, May 21, 2017

Shugaba Trump na Amurka zai saidawa Saudi makamai

An kulla yarjejeniyar makamai tsakanin Amurka da Kasar Saudiyya


 Shugaban kasar Amurka Trump ya kai ziyara kasar Saudi


– Kasashen sun shiga yarjejeniyar makamai na sama da Dala Biliyan 100


– Amurka da mukarabban ta na yaki a Yemen da ‘Yan Shi’a




Duk da irin maganganun da Donald Trump ya rika yi a baya abubuwa ba su canza ba. Kasar Amurka za ta cigaba da saidawa Saudiya manyan makaman yaki. Amurka dai ta nan ta ke samun makudan kudi.

Shugaba Donald Trump ya isa kasar Saudiya jiya inda aka kulla wata yarjejeniya na makamai na sama da Dala biliyan 110 wanda kuma nan da shekara goma za a kara sayan wasu na sama da Dala Biliyan 350.

Ba dai a ga maciji tsakanin Saudiya da kasar Iran, asali ma dai Saudiya na cigaba da yakar ‘Yan Houthi da ke Yemen wanda Kasar Iran ke marawa baya. Trump dai yana ma nema ya zarce Shugaba Obama wajen kawancan sa da kasar Saudiya.






[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...