Dagewa wajen neman halal-Daga Bakin Imam Dr. Saeed Muhammad Yunus
Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah,
Godiya ta tabbata ga Allah SWT tare da tsira da aminci ga Annabi SAW da
Alayen sa da Abokan sa da dukkan wadanda su ka bi hanyar sa zuwa ranar karshe.
Bayan haka, ‘Yan uwa mu sani cewa lallai addinin Musulunci, shi ne addinin bi.
Duk wanda ya bi Musulunci ya dace da rayuwa wanda ba ta da tabbas. Wanda ya
wayi gari cikin Musulunci shi ne ‘dan-gata!
Musulunci ya
kwadaitar da mu da aiki wajen neman halal, kuma duk inda Mutum zai tafi ya nemi
kudi, ya yarda matukar ba Haram bane. An tambayi Manzon Allah game da hakan,
sai yace ana iyawa. Ina maku wasiyya da kai na ‘Yan uwana, da mu ji tsoron
Allah. Ni’imomin Allah daga ciki akwai Musulunci, ka daina ganin Musulunci
karamin abu, babba ne! Da Allah ya so, da yanzu duk nan da mu ke Masallaci mu
na gidan giya. Allah ka kiyaye! Allah mun gode maka. Allah kai ka gusar mana da
damuwa na firgicin da mu ke ciki a kwanakin baya. Ya Allah Kai Ka sihirce mu
daga al’aura kamar yadda Hadisin ka na Kudusi ya fada. Ubangiji, mun san mu na ta
saba maka, da ka ga dama da Ka damke mu, amma Allah kace za ka jinkirta mana;
Mun san Ka yi wa Annabin mu alkawari cewa za ka dagawa Al’ummar sa kafa ba
kamar yadda ka yi wa Mutanen Annabi Lud ba, ba kamar yadda ka yi wa Mutanen
Salihu ko yadda ka yi wa Mutanen Hudu ko Mutanen Fira’una ba. Allah ka dagawa
Al’ummar Annabi Muhammadu kafa cewa su yi ta abin da su ka ga dama kuma kamu
yana nan zuwa Ranar kiyama. Allah ka da Ka kamu da abin da ba za mu iya ba!
‘Yan uwa mu sani
cewa Musulunci ya shar’antar da mu rika biyayya ga shugabanni da masu karanatar
da mu. Sun fada mana cewa lallai dukiya, abu ce wanda ake nema domin a ji dadi.
Muslunci ya kuma kwadaitar da neman kudi da kuma yadda za ka batar na tsarin
rayuwa. Daga ciki ne aka fitar da maganar zakka, amma Wawaye daga cikin mu, su
na gani cewa zakka tana rage dukiya. Annabawa da Manzanni sun taru gaba daya
cewa a tsarewa Mutane rayuwar su da dukiyar su da hankalin su da kuma mutuncin
su bayan tsare masu addinin su. Wajibi ne kowa ya sani cewa dukiya kawa ce ta
Duniya, cikin Al-Kur’ani, Suratul Kahfi tana cewa kudi da ‘ya ‘ya kawa ne na
Duniya. Wanda ya ki bada hakkin Allah ya shiga uku ya lalace.
Kudi abin kauna
ne, Musulunci bai ki kudi ba, Musulunci yana kaunar kudi; inda za a nemo na halal
a doron kasa a nemo na gina addini. ‘Yan uwa ku sani cewa mu na bukatar masu
kudi da za su taimaki addini, su gaskata abubuwan da Ubangiji ya fada na cewa
dukiya na d’aga al’amurra. Ubangiji na gyarawa da masu mulki abin da bai
gyarawa da masu ilmi haka kuma kudi na shiga inda ilmi bai shiga ba yayi aiki
na ban mamaki. Ku duba yadda Abubakar RA wanda ba shi aka ba Annabta ba, amma
yayi aiki da kudin sa. Sai ga shi Ubangiji yana fadar martabar Sa a Al-kur’ani.
Mu na bukatar masu dukiya; ku sani cewa dukiya makami ce, idan har ta shiga
hannun mabarnaci zai ta kashe mutane ne. Idan kuma ta shiga hannun Bawan Allah
kuma sai yayi ta gyara da ita kamar yadda Abubakar RA da Uthman RA da su
Abdurrahman bin Auf RA su ka yi da dukiyar su.
Ku duba yadda
Musab ya fito daga gidan kudi saboda Kalmar shahada. Wanda ake cewa ‘Dan Lu’u’lu’u
kamar yadda a wani zamani yaron Shugaban kasa ke cashewa cikin jirgi a sama.
Musab yana cikin irin wadannan, amma da ya ji kiran Manzon Allah, ya watsar da
wannan, sai ya dawo masallaci yana kwana. Sai ga Musab ya rasu a wajen jihadi ya
dawo bai da linkafani. Annabi bai da inda zai ajiye Musab amma sai ga Musab ana
saka masa ciyawa za a birne sa wanda Abdurrahman ‘Dan Auf da sauran Sahabbai su
ka rika kuka. Ku duba Uthman RA wanda ya auri ‘Ya ‘yan Manzon Allah har 2,
Annabi SAW yana cewa: Babu abin da Uthman zai kara mummuna a Duniya. ‘Yan uwa
idan dukiya ta fada hannun mugun mutum sai yayi barna kamar yadda Allah ya fada
a Al-Kur’ani yana cewa: ‘Ina amfanin wuta, mutum ya shiga wuta?’
‘Yan uwa mafi
girma daga cikin Musulmi shi ne wanda yake jin magana idan an fada masa. ‘Yan
uwa, kasala ba ta ga Musulmi ba. Musulunci ‘dan izza ne. ‘Yan uwa an ga
albarkar noma a Kasar mu. Kowa ya koma yaje yayi noma, a nemi halal! Manzon
Allah yana cewa a ci da halal kuma a nemi halal! A yi wa iyali hidima da halal,
ka da a ci haram. Ka da kuma ka raina halal duk yadda ta ke. Manzon Allah SAW yace
da Sa’ad bn Abi Waqqas da ya bar yaran sa da kudi ya fi ya bar su, su na roko.
Manzon Allah SAW yace ka da a kuma wulakanta wanda ake ciyarwa.
‘Dan uwa, wadanda
ke cewa Musulmi bai dace da neman dukiya ba macuta ne. Karya ce! Allah yace
babu wanda ya hana kawa ta Duniya. Allah yana so ka yi shiga mai kyau wanda
idan ka fita cikin Abokai za a ce kayi kyau. Ka sa riga ta daukaka ta buwaya da
kuma gidan ka mai kyau da abin hawan da ka ke da shi (keke ko babur) sannan
iyalin ka ma su sa mai kyau. Wani Sahabi ya tambayi Annabi SAW ya kuma fada
masa cewa wannan ba riya bane. Amma abin da Annabi SAW mai daraja ya fada shi
ne duk wanda ya sa tufafi yana mai girman kai, lallai Allah SWT sai ya sa masa
tufafi na kaskanci a gobe kiyama. ‘Yan uwa mu da iyalin mu, mu sa kaya masu
kyau. Yara su fito cikin Hijabi. Allah yace ku je ku nemi kudi a doron kasa.
Sayyidina Umar RA
ya taba fitowa sai ya ga wasu mutane sun zauna a gindin wata bishiya bayan
Sallar Juma’a. Da yace su wanene wadancan, sai su kace: Su masu tawakalli ne
kuma Allah Madaukaki kawai su ke jira ya ba su. Sayyidina Umar yana da wata
sanda da yake yawo da ita, sai ya bi ta kan su, ya kwala masu, yace ku fita ku
nema arziki, Musulunci ba ‘dan wulakanci bane. Umar yace ba ku ji Kur’ani yace
bayan Sallar ku, ku fita ku je ku nemi arziki ba. Ahmad ‘Dan Hambali (Allah
yayi masa rahama) bai yarda wani yayi dogaro da Allah ya tashi zuwa Garin
Makkah ba. ‘Dan Hambali yace ka fara neman guziri, sannan ka kama hanya, amma
idan guzuri ya kare, sai ka dogara da Allah. Sayyidina Umar ya hana ka zauna
kace Allah zai kawo arziki, yana cewa ai ka san sama ba ta ruwan zinari!
Huduba ta biyu
bayan godiya ga Allah da yabo ga Annabi SAW wanda ya sa mu ka zama mafificin Al’umma.
Allah ka kara masa daraja da wasila da fadila, Allah ka samu cikin haunin sa a
gobe kiyama. ‘Yan uwa ku sani cewa Musulunci ba addini bane na lalaci. Duk
wanda ya samu dukiya, amma bai yi abin da aka ce ba, ya lalace yayi asara. Tir da
wannan dukiya da ta kasance an sa ta inda ba ta dace ba. Malamai su na cewa
komai kankantar dukiya da aka yi abin da bai dace ba, an yi almubbazaranci.
‘Yan uwa mutane da
yawa a yau sun rabu dabam-dabam; akwai masu zaman benci su na gulmar
shugabanni, idan Malami mai arziki ya wuce a duba rigar sa. Idan wani Kamsila
ko wani ya wuce, su yi tayi da shi. Ba su da aikin yi sai zagin mutane.
Wadannan mutane ba su da komai sai zunubi. Annabi SAW yace a Ranar Kiyama, za a
nemi irin wadannan mutane su bada hakkin Majalisi. Huduba tana kiran Samari da
Dattawa cewa za a karbe ladar su, a ba wadannan, idan har ta kama, sai a dauki
aikin banzan wannan mutumi, a jefa maka. Wadannan mutane ba su fita nema, su na
ganin wani aikin bai dace da su ba; ba zai iya yin faskare ko yayi dako ba, ba
zai iya zuwa kasuwa ba, amma da kudi za su cika Masallacin nan, da su na gaba. Irin
wadannan mutane ne sai ka ji su na cewa da za su samu kudi, da sai sun fi
wane-da-wane kirki. Al-Kur’ani a Suratul Taubah ya fada mana ba haka ba. A
cikin su akwai wanda Allah ya jarabce sa yayi kudi na ban mamaki, amma da aka
saukar da ayar zakkah, sai yace domin sa aka saukar da ayar.
‘Yan uwa yau da
yawa daga cikin masu kudi su na kiyayya da zakkah. Wani ma da aka yi masa
lissafin zakkah sai yace ba gaskiya bane, wani kuma yana cewa dubarar Malamai
ce. Masu kudi ku sani cewa kun zo Duniya ba ku da komai. Ina kiran ku Wallahi
ku bada hakkin Allah, za ku bar baya da kura. ‘Yan kasuwa da masu sufuri na
fatauci da masu saida fetur da Jami’an hanya da Ma’aikatan Gwamnati da mai
saida taki a ji tsoron Allah. Kowa ya san irin abin da yake yi; duk dukiyar da
ka nema ko ka tara ba ta halal ba, kuma duk dukiyar da ka matsawa Musulmi ka
samu, ba za tayi albarka ba.
Wallahi Tallahi
kila ka taba jin wannan maganar, gobe za ka tsaya gaban Allah. Ba za ka iya cin
abin da ba rabon ka ba. ‘Yan uwa ku duba yadda aka rika kama Jama’a a cikin
Kasar nan sun saci dukiya. A kasar nan an rika kama beraye wanda su ka saci
dukiyar al’umma. Har iyaye mata da aka sani da rikon amana sun samu mukami, su
kayi cin amanar da ba a taba yi ba a tarihin wannan kasar. Dukiya ana neman ta
ne domin rufawa kai asiri amma ba ko ta wani hali ba. A lokacin da Sahabban
Manzon Allah su ka samu kudi, wasu sun rika kuka, su na cewa bala’i ya zo!
Akwai lokacin da bayan Sallah sai aka ga Annabi SAW ya fita a guje yana taba
kafadun mutane. Sahabbai su na ta mamaki, sai yace wata dukiya ce ya manta bai
ajiye ta inda ya kamata ba, sai ya kawo ya rabawa Jama’a.
‘Yan uwa ace
kullum kai ke nan maganar masu mukami, alhali kai ka gaza rike na ka mukamin da
aka ba ka. A kan abin da aka ba ka, za ayi maka tambaya a gobe kiyama. Ka da ka
raina abin da ka ke samu, ka zama mai godiya. Allah yayi alkawarin ba kowa bane
zai yi kudi don yace zai budawa wasu sannan kuma ya kuntatawa wasu, duk wanda
ba a ba sa ba, ya ciyar da daidai karfin sa. ‘Yan uwa ‘Yan Najeriya, yau haram
ta zama abin ado, an samu lokacin da yanzu wani yace: Wanda ya hana zalunci ma
Azzalumi ne! Wannan mummunan kalma ce! Annabin Rahma yace a nemi haram. Ko me
yake damun wadanda ke sa abinci su yi tsada? Ko wadanda aka ba amana su ci ta?
Me ke sa kananan yara su na satar kayan iyayen su? Samari sun ki karatu sun
buge da sata? Me ya sa mata ke sata a gidajen biki? Me ke damun al’umma ta rude?
Ko ina za a je ne? Ko ba mu bane al’ummar Annabi. Mu ne fa mu kace Allah ya
canza mana kuma ga shi ya canza. Ko har mun gaji ne? Inalillahi wa Inna ilaihi
Raji’un.
‘Yan uwa ku kara
naziri game da tafiyar Najeriya kamar yadda Saudiyya ta ke Garin Mutanen Annabi
Muhammad. Allah Mai Girma duk zai yi masu hisabi a gobe kiyama, Allah kuma ba
ya kallon daraja ko launin ko sai zuciyar ka. Kowa so yake ya samu dama a
Najeriya. Jini ya zama jinin sata, jijiya ta zama ta barayi; Jami’an tsaro na
jira ayi hadari su fara leka aljihun Jama’a. Kowane mataki ka shiga na karatu, za
ka samu Malamai da wannan hali. Wani yana Allah-Allah ya samu wata dama ya
dauke kayan ‘Dan uwan sa. Annabi yace: Babu ruwa na in ga wani a gobe kiyama da
akuyar sata. Ko karfen Masallacin nan ka sace, gobe sai ka zo da shi filin
kiyama.
‘Yan uwa mu bi a
hankali, hanzarin yayi yawa don kiyama ta kusa. Kiyama ta dosa amma mutane su
na cikin gafala. Annabi yace kiyamar nan ta kusa. Mu roki Allah ya kara mana
son Manzon Allah da zama cikin hakuri da tanadi da neman halal. Allah kuma ya
karawa masu dukiyar kirki albarka. Allah ya sa su ciyar da hakkin ka. Allah ka
sa mu zauna lafiya kayi mana maganin Barayi a kowane mataki. Allah ka sa masu
satar dukiya su daina ko ka canza mana su da wasu. Allah ka wahalar da wanda yake
so ‘yan kasa su wahala. Allah ka zaunar da mu lafiya. Allah ka kawo mana
karshen rikicin Benuwe da nan Kaduna da Jihohi dabam-dabam. Allah mun tuba da
laifin mu. Allah ka daidaita tsakanin Malaman Jihar Kaduna da Gwamnan su. Allah
ka jikan wadanda su ka riga mu gidan gaskiya. Allah ka sa kabarin mu ya zama
dausayin Aljannah. Ameen!
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Twitter: @Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment