Wednesday, January 24, 2018

That Baba OBJ's letter by M. Malumfashi



That Obasanjo’s letter… 

 


Like him or hate him, OBJ has been one man in this country who have won almost all the battles since 1960’s. It were his mates who staged the first coup and the counter months later. Colonel Obasanjo played a huge role in the Biafran war and even accepted the surrender of Biafran Army in 1970. He became the Chief of Staff SMC after Gowon was overthrown. Again, he ‘slightly’ missed Dimka’s bloody target in 1976, he made sure he didn’t miss Dimka after he became Head of State. After the Generals left the scene for politicians in 1979, Obasanjo was accused by Action Group’ Obafemi Awolowo of rigging elections for Shagari. Over 10 years later he and his Deputy were accused of staging a Coup and he particularly was pardoned and eventually came out alive. Abacha died mysteriously, and he OBJ was a President for years 8 straight, he couldn’t push beyond that! He installed a ‘sick’ ‘Yaradua (who died in 2010) and Jonathan Goodluck from nowhere. He was with Jonathan’s PDP before things changed, he wrote a letter like this time around, ‘Before it is too late’ and it was already too late then, for Jonathan. Obasanjo clearly supported the APC, nothing would have changed the 2015 story, but he won once again! General Muhammadu Buhari on the other hand fought many and won only one!

This week, Obasanjo sent a 13-page letter to the President, which must have left the APC calculating and the Presidency thinking. I don’t know if Obasanjo should in any way be Nigeria’s moral compass. At 78 he plays football on his birthday, went back to school for another Degrees, as if he is not responsible for the almost 12 years out of Nigeria’s post-independence mess. But he Obasanjo, must have said what many others including the President’s former staff have been saying and what the First family have been whispering from the other room! Obasanjo many not have the political base to decide 2019 but like always he must have calculated well. If one loves Buhari, I think it is time to listen for a while to this Grand Wailer!

Many hard-core Buharists have resorted to attacking Obasanjo instead of his words. They chose the messenger not the message! No one as at now have denied what Obasanjo said in his what seems now to be usual election year eve letters. As Buhari has the right to rule the Country till 80 years, Obasanjo has the right to speak at 80! All-in-all, the interesting thing said in the letter is that Buhari shouldn’t contest for another second term. Ironically, Obasanjo wanted a third term in office. Former President Obasanjo said the APC Government has tried it’s all and that is the best they could offer, this is the part where it’ll get some big APC men calculating the 2019 math. Obasanjo said he knew Buhari to be weak in Nation’s economics and foreign affairs policy and thought we will have looked for the best brains, he didn’t. Obasanjo may be had the best Economic team in history. Buhari’s Minister of budget is a Lawyer. They said the Minister of Finance went to a Polytechnic. What’s wrong with a Polytechnic! She was promoted from a ‘mere’ Commissioner to a non-coordinating Minister of the Economy. 

General Obasanjo said in his letter, the Economy doesn’t obey military order. Buhari his Junior in the Army tried to fix Naira-Dollar rates by sending DSS operatives arresting some Bureau D’ Change operators in 2015. In Obasanjo’s letter, he mentioned how the Economy danced to the tunes of our politics. Obasanjo thought the President will utilize the likes of his Professor Vice President who heads the Economic team. You don’t even need a political economist to be told that things are hard in the Country. Talking about foreign affairs policies, like many, I don’t much know about this administration’s policy. I only know that our Foreign affairs Minister used to have at least 5 pens in his pocket. Last time I read that so many Countries were waiting for Nigerian’ authority decisions on several issues, it took too long (like Ministers) to appoint Ambassadors. Nigeria’s Rep. to the United States, S. Nsofor is 82, older than the letter writer! Former President Obasanjo in his tenure traveled to 97 countries, Buhari had so many trips abroad to show too.

Ex-President Obasanjo mentioned about the President’s inability to discipline accused members of his circle, the case of Abdurrasheed Maina was an embarrassing example. This man was accused even by Jonathan’s Gov’t of corruption and was being wanted. Buhari’s Minister of Justice met Maina in Dubai, the next thing we had was that he has been back in office and even miraculously promoted. We have had enough stories of some power tussles in the Villa between the ever powerful Chief of Staff, SGF, EFCC boss, NSA, DSS and even the Head of service. Such has to the extent, embarrassed the President at the National Assembly. The failure to deal with such cases will forever leave a big blow on the face of the President. Someone puts it at ‘Buhari, you roared like a General, stop biting like a squirrel!’ 

There are some things that definitely have nothing to do with the price of crude barrel sold at $120, no blame games, fix things! In the letter, the Former President generously half-commended Buhari administration in the aspects of corruption and economy. When Obasanjo said the APC has nothing more to offer, then PDP (with one star man running the show) gives you some good options: Sule Lamido, Ayo Fayose, Ibrahim Shekarau, keep calling the names! It’s clear, Obasanjo doesn’t want another 2-times Leader to match his records, but I wonder how you get a Coalition of a-politicians or whatever that form and beat a sitting Government in a year!

Allah ya sa mu dace!

Muhammad Malumfashi is on Twitter @m_malumfashi

Wednesday, January 17, 2018

CAN, can you stop all this?


CAN, the 'Fulani' herdsmen and the Presidents

 


Before the 2015 elections, some Men of God threatened to open the gates of hell to anyone who opposed the President then – Goodluck Jonathan. The Christian Association endorsed Jonathan – who one of his loudest aides compared to Jesus Christ, for another tenure. At that time, the blood of thousands killed due to insecurity was at its highest boiling point. 

Boko Haram was at its peak in Nigeria, no need to say more on this. Under the man who he clearly failed to provide security for Nigeria and her citizens, not only in the North-Eastern Nigeria. The top Christian body and some followers then see Boko Haram as a Northern-Muslim agenda to prevent Jonathan from leading the Country. Boko Haram was only the doing of the terrorists and its victims, the President was never responsible for all they did, said the country’s constitution then.

Less than 4 years later today, we have another President who has evidently tried well to treat the Boko Haram terrorist with iron hands. Then there is the issue of herdsmen (the Fulanis as fondly called by our Media that has shown its own side), The Christian Association of Nigeria have now come out to blame the President, unlike 2012 or 2014, they now remember that the #1 is the Chief Security officer of the Nation and he should be sacked if he can’t protect Nigerians! The last time Boko Haram went out killing everyone, it was to make the Country ungovernable for the Southern President. The Herdsmen? They were only doing the bidding of their Master, the President himself, this time trying to make Nigeria ungovernable for himself with his tribe’s men, the Fulanis. 

When the Fulani’s strike hundreds dead in Zamfara, the CAN is silent, when it happens in Kaduna, it is because one El-Rufai is the Governor (who’s a hidden agenda like the President), when that happens in Benue, and the Governor’s name is Buhari – who doubles as the Commander-in-Chief. When there is a clash in the South; Rivers, Anambra or wherever, it is just some bad boys fighting over church or at worst family clash. When rival communities clash in Southern Kaduna, the CAN will say it’s because El-Rufai and the Imams wants to turn everyone to Muslim. The last time, CAN said they were the major victims of Boko Haram in a 99% Muslim dominated Borno.


Even when there is clear evidence that the Christian Association isn’t helping matters not only with their interpretations of statistics. In 2014, one jet was seized stacked with cash meant for weapons, after intervention of top Government officials, the jet was released by South African Government. The jet belongs to a father, Ayo Oritsejafor, the President wasn’t Muhammadu Buhari. An army officer, General Benjamin Ahanotu confirmed that there was indeed a massacre in Mambilla-Taraba State months ago. The General admitted that the State Government sponsored attacks on innocent young men and women. ‘I saw women, children and even animal hacked beyond description…’ He said. International press reported this. Recently, the Voice of America reported that the Benue State Government sponsored some militia parading as Civilian Joint task forces in the border of Benue and Taraba. This has been happening for over a year, one of the caught suspects in Arufu confessed. The Governor of Benue isn’t Nasir El-Rufai that one can accuse of sponsoring criminals. 

The Emir of Kano Sanusi II told Punch reporters about the genocide on Fulanis in Taraba State. He had pictures and evidences of pregnant women and the unborn slaughtered by Ethnic militants, the Fulani President failed to do anything about this, an attack on his dear tribesmen, like it’s happened in Zamfara, Jos, Numan, and Lau areas. Christian Association of Nigeria, after carrying its own extensive security inquiry this week discovered that the Emir was lying, again. There are evidences on the internet that the State Governor of Taraba ordered all the suspects arrested be released by the Police. There were many other panels constituted by the CAN with experts like Dr. Musa Asake, which came up with a report that all the investigations by the current IGP are false and he should be removed. This demand seems new however, it has not been the case when Arase was the Police head few months back. 

According to the Christian body, The Herdsmen are more dangerous than even Boko Haram. When the Nigerian Army visited Mambila, the Brigadier General who is from Southern part of the country said: …Boko Haram is not close to what I saw. Even at the time, the Army troops reached Mambilla, not only young Fulani men and women, even their cows were not left out, were burnt live. This barbaric act of ethnic cleansing never happened, according to the CAN. Can’t the CAN be responsible and call terrorists and criminals wherever they are, as one?



[Muhammad Malumfashi tweets at @m_malumfashi]





Saturday, January 13, 2018

HUDUBAR JUMA’A DAGA MIMBARIN ITN-ZARIA


Dagewa wajen neman halal-Daga Bakin Imam Dr. Saeed Muhammad Yunus

 

 

Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah, 




Godiya ta tabbata ga Allah SWT tare da tsira da aminci ga Annabi SAW da Alayen sa da Abokan sa da dukkan wadanda su ka bi hanyar sa zuwa ranar karshe. Bayan haka, ‘Yan uwa mu sani cewa lallai addinin Musulunci, shi ne addinin bi. Duk wanda ya bi Musulunci ya dace da rayuwa wanda ba ta da tabbas. Wanda ya wayi gari cikin Musulunci shi ne ‘dan-gata! 

Musulunci ya kwadaitar da mu da aiki wajen neman halal, kuma duk inda Mutum zai tafi ya nemi kudi, ya yarda matukar ba Haram bane. An tambayi Manzon Allah game da hakan, sai yace ana iyawa. Ina maku wasiyya da kai na ‘Yan uwana, da mu ji tsoron Allah. Ni’imomin Allah daga ciki akwai Musulunci, ka daina ganin Musulunci karamin abu, babba ne! Da Allah ya so, da yanzu duk nan da mu ke Masallaci mu na gidan giya. Allah ka kiyaye! Allah mun gode maka. Allah kai ka gusar mana da damuwa na firgicin da mu ke ciki a kwanakin baya. Ya Allah Kai Ka sihirce mu daga al’aura kamar yadda Hadisin ka na Kudusi ya fada. Ubangiji, mun san mu na ta saba maka, da ka ga dama da Ka damke mu, amma Allah kace za ka jinkirta mana; Mun san Ka yi wa Annabin mu alkawari cewa za ka dagawa Al’ummar sa kafa ba kamar yadda ka yi wa Mutanen Annabi Lud ba, ba kamar yadda ka yi wa Mutanen Salihu ko yadda ka yi wa Mutanen Hudu ko Mutanen Fira’una ba. Allah ka dagawa Al’ummar Annabi Muhammadu kafa cewa su yi ta abin da su ka ga dama kuma kamu yana nan zuwa Ranar kiyama. Allah ka da Ka kamu da abin da ba za mu iya ba! 

‘Yan uwa mu sani cewa Musulunci ya shar’antar da mu rika biyayya ga shugabanni da masu karanatar da mu. Sun fada mana cewa lallai dukiya, abu ce wanda ake nema domin a ji dadi. Muslunci ya kuma kwadaitar da neman kudi da kuma yadda za ka batar na tsarin rayuwa. Daga ciki ne aka fitar da maganar zakka, amma Wawaye daga cikin mu, su na gani cewa zakka tana rage dukiya. Annabawa da Manzanni sun taru gaba daya cewa a tsarewa Mutane rayuwar su da dukiyar su da hankalin su da kuma mutuncin su bayan tsare masu addinin su. Wajibi ne kowa ya sani cewa dukiya kawa ce ta Duniya, cikin Al-Kur’ani, Suratul Kahfi tana cewa kudi da ‘ya ‘ya kawa ne na Duniya. Wanda ya ki bada hakkin Allah ya shiga uku ya lalace. 

Kudi abin kauna ne, Musulunci bai ki kudi ba, Musulunci yana kaunar kudi; inda za a nemo na halal a doron kasa a nemo na gina addini. ‘Yan uwa ku sani cewa mu na bukatar masu kudi da za su taimaki addini, su gaskata abubuwan da Ubangiji ya fada na cewa dukiya na d’aga al’amurra. Ubangiji na gyarawa da masu mulki abin da bai gyarawa da masu ilmi haka kuma kudi na shiga inda ilmi bai shiga ba yayi aiki na ban mamaki. Ku duba yadda Abubakar RA wanda ba shi aka ba Annabta ba, amma yayi aiki da kudin sa. Sai ga shi Ubangiji yana fadar martabar Sa a Al-kur’ani. Mu na bukatar masu dukiya; ku sani cewa dukiya makami ce, idan har ta shiga hannun mabarnaci zai ta kashe mutane ne. Idan kuma ta shiga hannun Bawan Allah kuma sai yayi ta gyara da ita kamar yadda Abubakar RA da Uthman RA da su Abdurrahman bin Auf RA su ka yi da dukiyar su. 

Ku duba yadda Musab ya fito daga gidan kudi saboda Kalmar shahada. Wanda ake cewa ‘Dan Lu’u’lu’u kamar yadda a wani zamani yaron Shugaban kasa ke cashewa cikin jirgi a sama. Musab yana cikin irin wadannan, amma da ya ji kiran Manzon Allah, ya watsar da wannan, sai ya dawo masallaci yana kwana. Sai ga Musab ya rasu a wajen jihadi ya dawo bai da linkafani. Annabi bai da inda zai ajiye Musab amma sai ga Musab ana saka masa ciyawa za a birne sa wanda Abdurrahman ‘Dan Auf da sauran Sahabbai su ka rika kuka. Ku duba Uthman RA wanda ya auri ‘Ya ‘yan Manzon Allah har 2, Annabi SAW yana cewa: Babu abin da Uthman zai kara mummuna a Duniya. ‘Yan uwa idan dukiya ta fada hannun mugun mutum sai yayi barna kamar yadda Allah ya fada a Al-Kur’ani yana cewa: ‘Ina amfanin wuta, mutum ya shiga wuta?’

‘Yan uwa mafi girma daga cikin Musulmi shi ne wanda yake jin magana idan an fada masa. ‘Yan uwa, kasala ba ta ga Musulmi ba. Musulunci ‘dan izza ne. ‘Yan uwa an ga albarkar noma a Kasar mu. Kowa ya koma yaje yayi noma, a nemi halal! Manzon Allah yana cewa a ci da halal kuma a nemi halal! A yi wa iyali hidima da halal, ka da a ci haram. Ka da kuma ka raina halal duk yadda ta ke. Manzon Allah SAW yace da Sa’ad bn Abi Waqqas da ya bar yaran sa da kudi ya fi ya bar su, su na roko. Manzon Allah SAW yace ka da a kuma wulakanta wanda ake ciyarwa. 

‘Dan uwa, wadanda ke cewa Musulmi bai dace da neman dukiya ba macuta ne. Karya ce! Allah yace babu wanda ya hana kawa ta Duniya. Allah yana so ka yi shiga mai kyau wanda idan ka fita cikin Abokai za a ce kayi kyau. Ka sa riga ta daukaka ta buwaya da kuma gidan ka mai kyau da abin hawan da ka ke da shi (keke ko babur) sannan iyalin ka ma su sa mai kyau. Wani Sahabi ya tambayi Annabi SAW ya kuma fada masa cewa wannan ba riya bane. Amma abin da Annabi SAW mai daraja ya fada shi ne duk wanda ya sa tufafi yana mai girman kai, lallai Allah SWT sai ya sa masa tufafi na kaskanci a gobe kiyama. ‘Yan uwa mu da iyalin mu, mu sa kaya masu kyau. Yara su fito cikin Hijabi. Allah yace ku je ku nemi kudi a doron kasa. 

Sayyidina Umar RA ya taba fitowa sai ya ga wasu mutane sun zauna a gindin wata bishiya bayan Sallar Juma’a. Da yace su wanene wadancan, sai su kace: Su masu tawakalli ne kuma Allah Madaukaki kawai su ke jira ya ba su. Sayyidina Umar yana da wata sanda da yake yawo da ita, sai ya bi ta kan su, ya kwala masu, yace ku fita ku nema arziki, Musulunci ba ‘dan wulakanci bane. Umar yace ba ku ji Kur’ani yace bayan Sallar ku, ku fita ku je ku nemi arziki ba. Ahmad ‘Dan Hambali (Allah yayi masa rahama) bai yarda wani yayi dogaro da Allah ya tashi zuwa Garin Makkah ba. ‘Dan Hambali yace ka fara neman guziri, sannan ka kama hanya, amma idan guzuri ya kare, sai ka dogara da Allah. Sayyidina Umar ya hana ka zauna kace Allah zai kawo arziki, yana cewa ai ka san sama ba ta ruwan zinari!

Huduba ta biyu bayan godiya ga Allah da yabo ga Annabi SAW wanda ya sa mu ka zama mafificin Al’umma. Allah ka kara masa daraja da wasila da fadila, Allah ka samu cikin haunin sa a gobe kiyama. ‘Yan uwa ku sani cewa Musulunci ba addini bane na lalaci. Duk wanda ya samu dukiya, amma bai yi abin da aka ce ba, ya lalace yayi asara. Tir da wannan dukiya da ta kasance an sa ta inda ba ta dace ba. Malamai su na cewa komai kankantar dukiya da aka yi abin da bai dace ba, an yi almubbazaranci. 

‘Yan uwa mutane da yawa a yau sun rabu dabam-dabam; akwai masu zaman benci su na gulmar shugabanni, idan Malami mai arziki ya wuce a duba rigar sa. Idan wani Kamsila ko wani ya wuce, su yi tayi da shi. Ba su da aikin yi sai zagin mutane. Wadannan mutane ba su da komai sai zunubi. Annabi SAW yace a Ranar Kiyama, za a nemi irin wadannan mutane su bada hakkin Majalisi. Huduba tana kiran Samari da Dattawa cewa za a karbe ladar su, a ba wadannan, idan har ta kama, sai a dauki aikin banzan wannan mutumi, a jefa maka. Wadannan mutane ba su fita nema, su na ganin wani aikin bai dace da su ba; ba zai iya yin faskare ko yayi dako ba, ba zai iya zuwa kasuwa ba, amma da kudi za su cika Masallacin nan, da su na gaba. Irin wadannan mutane ne sai ka ji su na cewa da za su samu kudi, da sai sun fi wane-da-wane kirki. Al-Kur’ani a Suratul Taubah ya fada mana ba haka ba. A cikin su akwai wanda Allah ya jarabce sa yayi kudi na ban mamaki, amma da aka saukar da ayar zakkah, sai yace domin sa aka saukar da ayar. 

‘Yan uwa yau da yawa daga cikin masu kudi su na kiyayya da zakkah. Wani ma da aka yi masa lissafin zakkah sai yace ba gaskiya bane, wani kuma yana cewa dubarar Malamai ce. Masu kudi ku sani cewa kun zo Duniya ba ku da komai. Ina kiran ku Wallahi ku bada hakkin Allah, za ku bar baya da kura. ‘Yan kasuwa da masu sufuri na fatauci da masu saida fetur da Jami’an hanya da Ma’aikatan Gwamnati da mai saida taki a ji tsoron Allah. Kowa ya san irin abin da yake yi; duk dukiyar da ka nema ko ka tara ba ta halal ba, kuma duk dukiyar da ka matsawa Musulmi ka samu, ba za tayi albarka ba. 

Wallahi Tallahi kila ka taba jin wannan maganar, gobe za ka tsaya gaban Allah. Ba za ka iya cin abin da ba rabon ka ba. ‘Yan uwa ku duba yadda aka rika kama Jama’a a cikin Kasar nan sun saci dukiya. A kasar nan an rika kama beraye wanda su ka saci dukiyar al’umma. Har iyaye mata da aka sani da rikon amana sun samu mukami, su kayi cin amanar da ba a taba yi ba a tarihin wannan kasar. Dukiya ana neman ta ne domin rufawa kai asiri amma ba ko ta wani hali ba. A lokacin da Sahabban Manzon Allah su ka samu kudi, wasu sun rika kuka, su na cewa bala’i ya zo! Akwai lokacin da bayan Sallah sai aka ga Annabi SAW ya fita a guje yana taba kafadun mutane. Sahabbai su na ta mamaki, sai yace wata dukiya ce ya manta bai ajiye ta inda ya kamata ba, sai ya kawo ya rabawa Jama’a. 

‘Yan uwa ace kullum kai ke nan maganar masu mukami, alhali kai ka gaza rike na ka mukamin da aka ba ka. A kan abin da aka ba ka, za ayi maka tambaya a gobe kiyama. Ka da ka raina abin da ka ke samu, ka zama mai godiya. Allah yayi alkawarin ba kowa bane zai yi kudi don yace zai budawa wasu sannan kuma ya kuntatawa wasu, duk wanda ba a ba sa ba, ya ciyar da daidai karfin sa. ‘Yan uwa ‘Yan Najeriya, yau haram ta zama abin ado, an samu lokacin da yanzu wani yace: Wanda ya hana zalunci ma Azzalumi ne! Wannan mummunan kalma ce! Annabin Rahma yace a nemi haram. Ko me yake damun wadanda ke sa abinci su yi tsada? Ko wadanda aka ba amana su ci ta? Me ke sa kananan yara su na satar kayan iyayen su? Samari sun ki karatu sun buge da sata? Me ya sa mata ke sata a gidajen biki? Me ke damun al’umma ta rude? Ko ina za a je ne? Ko ba mu bane al’ummar Annabi. Mu ne fa mu kace Allah ya canza mana kuma ga shi ya canza. Ko har mun gaji ne? Inalillahi wa Inna ilaihi Raji’un. 

‘Yan uwa ku kara naziri game da tafiyar Najeriya kamar yadda Saudiyya ta ke Garin Mutanen Annabi Muhammad. Allah Mai Girma duk zai yi masu hisabi a gobe kiyama, Allah kuma ba ya kallon daraja ko launin ko sai zuciyar ka. Kowa so yake ya samu dama a Najeriya. Jini ya zama jinin sata, jijiya ta zama ta barayi; Jami’an tsaro na jira ayi hadari su fara leka aljihun Jama’a. Kowane mataki ka shiga na karatu, za ka samu Malamai da wannan hali. Wani yana Allah-Allah ya samu wata dama ya dauke kayan ‘Dan uwan sa. Annabi yace: Babu ruwa na in ga wani a gobe kiyama da akuyar sata. Ko karfen Masallacin nan ka sace, gobe sai ka zo da shi filin kiyama. 

‘Yan uwa mu bi a hankali, hanzarin yayi yawa don kiyama ta kusa. Kiyama ta dosa amma mutane su na cikin gafala. Annabi yace kiyamar nan ta kusa. Mu roki Allah ya kara mana son Manzon Allah da zama cikin hakuri da tanadi da neman halal. Allah kuma ya karawa masu dukiyar kirki albarka. Allah ya sa su ciyar da hakkin ka. Allah ka sa mu zauna lafiya kayi mana maganin Barayi a kowane mataki. Allah ka sa masu satar dukiya su daina ko ka canza mana su da wasu. Allah ka wahalar da wanda yake so ‘yan kasa su wahala. Allah ka zaunar da mu lafiya. Allah ka kawo mana karshen rikicin Benuwe da nan Kaduna da Jihohi dabam-dabam. Allah mun tuba da laifin mu. Allah ka daidaita tsakanin Malaman Jihar Kaduna da Gwamnan su. Allah ka jikan wadanda su ka riga mu gidan gaskiya. Allah ka sa kabarin mu ya zama dausayin Aljannah. Ameen!





Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Muhammadmalumfashi@gmail.com          
Twitter: @Ya_waliyyi








Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...