Hudubar Juma’a daga Mimbarin ITN-Zaria
‘Hudubar Juma’a game da harkar Ilmi a ban kasa da Jihar Kaduna -Daga Bakin Imam Ustaz Sa’eed Yunus.
Assalamu Alaikum wa Rahmatul
Lah,
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah SWT, tsira da amincin Allah su tabbata ga wanda babu Annabi
bayan sa, Shugaban mu, kuma Annabin mu, farin Jakadar Allah; Annabi Muhammadu
SAW, tare da iyalan sa da Sahaban sa tare da duk wadanda suka bisa da
kyautatawa zuwa har Ranar karshe.
Bayan haka, mu sani cewa mu na
cikin wani lokaci da mu ka shiga cikin wani hali a ban kasa. Babu abin da ya
jawo wannan sai rashin karatu da neman ilmi.
Ilmin da ya kamata a maida
hankali a kai sun hada da: Na farko, dole a komawa Al-Kur’ani, ayi aiki da shi
ana tadabburi kuma tare da haddacewa kamar yadda Allah ya fada. Sannan kuma
ilmin fassara Al-Kur’ani watau Hadisan Manzon Allah SAW. Sannan kuma ilmi na
Akida wanda ke fitar da mutum daga sharrin shirka. Sannan kuma da ilmin nan na
Fikihu. ‘Yan uwa masu girma ilmi yana da yawa; daga ciki har da ilmi na harshen
larabci wanda za ayi magana da shi a gobe kiyama gaban Allah SWT. Da yaren larabci
aka saukar da Al-Kur’ani. Daga cikin ilmin da ya kamata a ba muhimmanci akwai
ilmin kimiyya, tattali da kuma shari’a da kuma ilmi na koyan Malanta. Duk wani
ilmi ya kamata ace an samu Musulmi a wannan wuri. Daga cikin ilmi masu amfani
kuma akwai ilmi na aikin Soja wanda za a juya duk wani makami wanda za a kare
addini kamar yadda Al-Kur’ani yake cewa ku yi tanadi na kare kai! Ana bukatar
masu tare wurare na harba bam domin kare addini a kuma kare kasa da manyan
kasa. Yanzu wadannan mabarnata masu garkuwa da mutane a kasa, ya kamata ace an
samu ilmin da zai kawo karshen su.
Huduba tana kuma kira gare ku
da a samu ikhlasi watau tsarkin niyya. Idan aka ce kai Injiniya ne, to ka zama
Musulmin Injiniya, ko kuma ace kai Musulmi ne kuma Likita ko kuma Soja ko
Malamin Makaranta ko kuma Makanike ko mai aiki a Kamfani amma Musulmi. Kuma don
Allah duk wadanda za su rubuta wani abu da Dalibai su ke amfani da shi su ji
tsoron Allah. Wallahi idan har ka sa abin da kuma zai bata tarbiyyar yara za
kayi bayani a Ranar tashin kiyama ka gane kuren ka. Ku san irin Makarantun
Bokon da za ku sa yaran ku; wasu iyayen su na jefa yaran su cikin tabo sannan
kuma su na cewa ka da yaran su jike, wannan hauka ne! Sai ka ga mutum ya dauki
diyar sa ya kai wurin wadanda ba Musulmi ba. Saboda haka yana da kyau mu gyara
don kuwa za a tambaye ku a gobe kiyama.
Sannan kuma Malaman Makaranta
ku ji tsoron Allah don ku na da hakki da kuma abin da za su ku fada. Hudubar yau
tana jinjinawa Malamai, ina gaishe ku Malaman Makaranta. Malaman Makarantar
Gwamnati ba wanda yake koyarwa a Makarantun kasuwa ba. Ni ina ce maku ‘Salamu
Alaikum’ don kun cancanci gaisuwa, ku ne Malamai na gaskiya kuma na san aikin
da ku ke yi. Kun cancanci a ba ku tukwuici a duk matakin da ku ke na firamare
ko sakandare balle ma kuma Jami’a uwa-uba.
Amma kuma abin bakin ciki sai
aka samu irin wannan tafiyar a yau ta tabarbare. An samu wasu da su ka je su ka
koyi karatu daga kwaleji ko FCE kuma su ke karantarwa da kyau. Wasu kuma sun
shiga hakkin yara; ba a shiga aji ba kuma a kula da yara. Malamai ku ji tsoron
Allah, wannan abin shi ya jawo bala’in da aka shiga a Jihar Kaduna, Allah kadai
ne zai yi hukunci gobe a kiyama, wannan abun bakin ciki ne. Allah shi kadai ne
mai cikar kamala don babu wanda za ayi wa jarrabawa a ce sai ya ci
dari-bisa-dari, amma kun ci amanar kasar ku gaba daya. A makarantun na fa kitso
ake yi da sayar da atamfa, kungiyoyi su yi ta kawo tallace-tallace. Sai yara su
tafi Makaranta amma ba ayi masu komai ba! Shekara nawa aka yi ana wannan abu?
Wallahi ya fi shekaru 30 ana haka! Wadanda su ka sani sun sani, wadanda ba su
sani ba, sun jahilta. Wannan itace al’adar Malamai (ba na Jihar Kaduna ba
kurum). Idan aka ce a Kaduna kadai ake wannan an zalunci Malaman Jihar, kusan
kaf Najeriya ta Arewa shekaru 30 da su ka wuce Malamai kan yi wasa da aikin su.
Sannan kuma aka samu Gwamnoni da su ka rika daukar mutanen da su ka cancanta da
wadanda ba su cancanta ba, an maida karantawar kamar bola. Lokaci ya kai ana kawo
wadanda ba Malamai ba amma su na koyarwa ba tare da sun san komai ba su na
karanatar da yara!
‘Yan uwa ku ba ni labarin
wadanda aka kama bayan shigowar Gwamnatin Shugaba Buhari su na da ‘ya ‘ya a gida
amma ana ba su albashi. Sai ka ga mutum da matan sa 4 da ‘ya ‘ya 24 amma kowane
yana samun albashi a karshen wata. Tsakani ga Allah ba canji ku ka nema ba? Kun
nemi canji sai Allah ya kawo maku, sai kuma ku ce ba ku yarda ba? Ka na bakin
ciki don an kama ‘Dan uwan ka da laifi ba ya shiga aji? ‘Dan uwan ka ya ci
amanar hukuma, ba gara ya zama an kama sa tun a Duniya ba a kafin ya isa lahira
ya ji kunya? Saboda haka ku ji tsoron Allah, abin da baki ya fada zai iske shi
a gobe kiyama.
Annabawan Allah sun yi
gwagwarmya; Annabi Musa AS yayi fama da Fir’auna; Bani Israila sun kai kuka
cewa ana kashe su har Allah ya kashe Fir’auna, sai ga shi wadannan mutane sun
kuma nemi a kera masu gunki. Annabi Musa AS yace wadannan mutane ba su fahimci
abubuwa ba. Ko su ku ke mu ma ayi shekara 40 ana yi mana azaba? Annabi Muhammad
SAW ma dai bai kubuta ba don har ta kai Sahaban sa sun nemi Allah ya kawo yaki
yayin da aka umarce su da su yi ta sallah. Sai ga shi a lokacin da aka hukunta
yaki su na jin tsoro su na cewa meyasa aka ce su fita yaki. Jama’a ku kuce ‘Mai
Rusau, Mai Rusau!’Ga shi kuma ya zo ya rusa kuma yana ta rusawa kuma kun ce ba
ku yarda ba! Ku na so ku shekara 40 kenan a wulakance? Wallahi ba kamfe bane! Wallahi
ba kamfe bane! Wallahi ba kamfe bane! Gaskiya ce dole kuma a fada!
Ko kun ki ko kun so wanda ya
gama Gwamna abin yabo ne amma ku ka zage sa, ga shi kuma Allah ya kawo wannan.
Abin bakin ciki shi ne a kan Musulmi duk tsinuwar ta ke karewa; Musulmi ke
zagin ‘Dan uwan sa. A karatun da Malam yayi, yake cewa idan tsinuwar ba ta hau
kan sa ba za ta hau kan ku kuma sai ta tafarfasa ku. Shiyasa mu na nan mun kasa
cigaba har yanzu. Al-Kur’ani ya fada mana cewa; Allah ya kama Fir’auna da
Hamana da duk masu laifi. ‘Yan uwan ku kiyaye wannan kamun na Allah.
Huduba tana rokon Allah ya
azurta mu da ilmi mai amfani. Ina neman gafara gare ku ‘Yan uwa. Sannan bayan
godiya ga Allah huduba tana cewa Jama’a ku ji tsoron Allah, ku kiyayi ha’inci
na jarrabawa da ake yi, ku kiyayi kai yara Makarantun da ake kira Miracle Centres da ake cin jarrabawa,
karya ne munafunci ne. Yaran Musulmai su ka cika wadannan Makarantu alhali su su
na Makarantun Gwamnati. Makarantun nan na Gwamnati su ne Makarantun asali,
lalata su aka yi. Sai ace wai Shugabanni sun ki kai yaran su Makarantun
Gwamnati, ku ina ku kai na ku yaran? Ka yarda cewa diyar ka ta je Makaranta da
hijabi na Sunnah amma daga ta isa bakin Makaranta sai ace ta tube? Mun dauki
amanar yaran mu, mun kai wurin wadanda ba mu ba! Wannan fa shi ne yake ba ta
tarbiyya, wanda bai da abu ba zai ba da shi ba.
Ku Malamai na Jihar Kaduna ku
gyara al’amarin ku, ku ji tsoron Allah. Wasu ne su ka jawo maku wannan bala’i,
ba laifin ku ba ne duka Wallahi! Idan ka shiga Jami’ar Ahmadu Bello za ka ji ba
za ka iya kwashe ‘Daliban da su kayi jarrabawar kwanan nan ba. Kuma ku duba Daliban
da aka fitar zuwa Kasar Uganda domin karatun likitanci amma an dawo da su, meya
faru? Duk wadannan mugayen Makarantu su kayi. Amma kun tambayi tarihi mana.
Don haka ina kira ga Hukuma ta
ilmi da duk wani mai ta cewa, ni dai na fadi nawa a matsayi na ‘Dan uwan ku
Musulmi; Malaman nan da aka kora a duba al’amarin su, ya ku Gwamnati, ka da ku
kori Malamai. Amma duk wanda ya kasance ba Malami bane, ba na goyon bayan a
cigaba da tafiya da shi. Ina kira ga Gwamnati don Allah a ba su hakkin su.
Malaman nan fa Malamai ne ba za a hada su da wadannan yara ba da ake shirin
dauka Wallahi! Ku yi hakuri, da tsohuwar zuma ake magani. A gyara su ne kawai.
Ku kuma Malamai ku iya bakin
ku, ku tuna da Hadisin Manzon Allah da ya ga wasu ana yanka bakunan su da lauje
a kabari, da Manzon Allah ya tambaya a kan su sai aka fada masa cewa su ne masu
fadar abin da ba su sani ba. Kun zagi wancan Gwamnan, kun zagi Gwamnan da ya
wuce, wanda ya wuce ya zama Sanata kun tsine masa, gobe kiyama sai ka fadi abin
da Gwamna yayi maka! Tsoho Baba Buhari wadansu har sun fara zagin sa, shi ma ma
sai ka fadi abin da yayi maka a gobe kiyama. Ka kiyayi bakin ka Musulmi don duk
baki ya jawo mana wannan.
Mu tambayi tarihin su Sardauna
da su Tafawa-Balewa wadanda su ka jawowa kasa izza amma yanzu an jawo mana
zilla. Idan ba mu bane da mulkin kasar nan sai ka ji bakin Jama’a shiru, amma
daga na mu ya samu sai ka ji ana ta ‘Allah ya tsine.’ Ka sani babu abin da za
ka samu saboda wani Gwamna ko yanayi. Matsalar tamu ce mu kan mu, kuma sai an
tambaye mu a kiyama.
Huduba tana cewa lallai ku
kiyayi ka-ce-na-ce watau kila-wa-kala, ku kiyayi mugun zato ga Musulmi. A kuma
daina zagin Shugabanni, a daina tsinewa Malamai, kiyayi zunubi da sabon Allah
wanda shi ya jawo mana wannan bala’i. Yau ba mu da Soja mai gaskiya; barikin
nan na Zariya an koro yaran mu sama da 800 don ba su da takardun shaida. Meya
faru? Sun je Miracle Centers domin
jarrabawa. Ga su nan a Jami’a kuma; a dalilin rashin Jarrabawar nan na Post UTME yanzu an yi jarrabawar aji daya
duk sun fadi saboda ba a tace ba, su ma sun je Miracle Centers.
Iyaye ku ji tsoron Allah ku samawa yaran ku Makarantu
na gaskiya. Lauyoyin mu, ku zama masu fadar gaskiya. Likitocin mu ku ji tsoron
Allah, ilmin ku yayi amfani. Ya kai mai neman Shugabanci ka ji tsoron Allah. Ka
sani cewa kabari na nan yana jira. Ya kai wawa wanda ka rafkana, ka dauki
Duniya wajen zama, ya kai Saurayi da ka ke ganin za ka dade, Ya kai Shugaba da
ka ke danne hakkin Jama’a, ya kai da ake shugabanta da ka ke zagin Shugabanni,
duk ku sani cewa akwai tsayuwa gaban Allah kuma akwai kabari. Wallahi kabari
sama turbaya ne kasan sa babu wanda ya sani sai Allah! Yau ga shi ka mutu kai
ne mai surutu a wata Majalisa.
Allah ya hada mu cikin masu
son gaskiya da riko da gaskiya da aiki da gaskiya. Allah ya sa kabari wajen
hutawar mu ne. Allah ka sa mu karbi littafin mu da hannun dama. Allah ka
taimaki Shugabannin mu na kirki, wadanda ba za su gyaru ba ka canza mana su.
Allah ka biyawa kowa bukatan sa mazan mu da matan mu!
[Akwai
wasu sashe na hudubar Malam da su ka shafe daga na’ura]
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga
Masallacin I.T.N-Zaria. Muhammadmalumfashi@gmail.com Twitter:@Ya_waliyyi