Friday, September 8, 2017

Wani ya auri bera bayan mutuwar matar sa

Wani mutumi ya auri bera a Kasar India

 



A Kasar India wani ya auri bera bayan mutuwar matar sa

Mista Basu yana ganin matar sa ce ta dawo a jikin bera

Bawan Allan ya rasa matar sa ne a hadarin mota kwanaki




Mun samu labari na musamman cewa wani ya auri bera bayan mutuwar matar sa a can kasar India a Watan Junairu.

Wani mutumi mai suna Chidhatma Basu ya auri macen bera a Garin Bangalore na Kasar India bayan mai dakin sa ta rasu a farkon shekarar nan a wani hadarin mota. Mutuwar ta sa wannan mutumi mai shekaru 41 da 'ya 'ya 4 ya zama gwauro.

Mista Basu yace wata rana yana zaune cikin takaici da maraici sai ga shi ya ga wata bera mai idanuwa da hanci sak na marigayiyar matar sa. Mutumin yace ya fahimci cewa matar sa ce kurum ta dawo daga irin abincin da take ci. Malamin da ya daura auren yace tabbas haka aka yi.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...