A Kasar India wani ya auri bera bayan mutuwar matar sa
Mista Basu yana ganin matar sa ce ta dawo a jikin bera
Bawan Allan ya rasa matar sa ne a hadarin mota kwanaki
Mun samu labari na
musamman cewa wani ya auri bera bayan mutuwar matar sa a can kasar India a Watan Junairu.
Wani mutumi mai suna
Chidhatma Basu ya auri macen bera a Garin Bangalore na Kasar India bayan mai
dakin sa ta rasu a farkon shekarar nan a wani hadarin mota. Mutuwar ta sa
wannan mutumi mai shekaru 41 da 'ya 'ya 4 ya zama gwauro.
Mista Basu yace wata
rana yana zaune cikin takaici da maraici sai ga shi ya ga wata bera mai idanuwa
da hanci sak na marigayiyar matar sa. Mutumin yace ya fahimci cewa matar sa ce
kurum ta dawo daga irin abincin da take ci. Malamin da ya daura auren yace
tabbas haka aka yi.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment