HDUBAR JUMA'A DAGA MASALLACIN ITN
Daga bakin Sheikh Dr. Saeed Yunus Zaria
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wa barakatuhu
Dukkan
yabo da godiya su tabbata ga Allah, muna gode masa mu na neman taimakon Sa, mu na
neman gafarar Sa muna tuba gare Shi.
Mu
na neman tsari daga sharrin kawunan mu, da kuma munanan ayyukan mu, duk wanda Allah
ya shiryar da shi babu wanda ya isa ya batar da shi. Duk wanda Allah ya batar
da shi ya bace babu mai iya shiryar da shi.
Allah ka shirye mu!
Muna
shaidawa babu abin bauta face Allah shi kadai, kuma mu na shaidawa Annabin mu
mosoyin mu Muhammad SAW (Farin Jakadan Allah) tsira da amincin Allah su tabbata
gare shi Bawan Allah ne, kuma Manzon Allah ne, Allah ka dada tsira da aminci ga Annabin sa, Annabi Muhammad (SAW) da Alayan
Sa, da Sahabban Sa.
Bayan
haka ‘Yan uwa mu ji tsoron Allah mu siffantu da siffofi irin na Al-Kurani.
Lallai Annabi ya kasance halayansa Al-Kurani ne, idan kana so ka kalli Kurani, ka
kalli rayuwar Manzon Allah SAW. Annabi yana nisantar duk wani hani na Kurani,
yana tafiya da duk wani umurni na Kur’ani, kuma shi Kur’ani shine shiriya ga
dukkan mutane. Allah ya shiryar da annabi ta hanyar Kur’ani, don haka Annabi ya
cigaba da tafiya akan wannan hanyar ta Kurani. Annabi yayi hakane (kamar yadda
Allah umarce shi) don ya fitar da mutane daga duhu zuwa haske. Lallai Kur’ani Ambato
ne wanda Allah ya saukar da shi mai hikima, mai dadi, kuma hanyar Allah ce. Kur’ani
yana shiryar da mutane zuwa ga hanya madaidaiciya, duk inda aka bi Duniya da Lahira
yana shiryar da mutane kan hanya da take mafi tsayuwa a cikin umarni da hani,
da kuma rayuwa da kwanciyar hankali.
Daga
cikin karantarwar addinin Musulunci da karantarwar Kur’ani ‘Yan uwa akwai abubuwan
da Allah ya ambata dangane da Iyayenmu Mata; Matan shugaban tafiya watau Annabi
Muhammad SAW, sannan inda Allah a cikin Kur’ani Ya nuna tsarkakar Matan Annabi
Muhammad SAW. Matan Annabi tsarkakakku ne, wanda ya zage su ya tabe, wanda ya
zagi daya daga cikin su ya tabe Duniya da Lahira, saboda Allah ya tsarkake su,
Allah ya ambace su a matsayin Muminai masu da’a ga Allah. Allah ya kira Matan Manzon
Sa da cewa “Watau ku zauna a cikin dakunan
ku yaku matan Manzon Allah kada kuyi fita irin ta matan jahiliyya ta farko”,
fitan tsaraici ku sani cewa bayan an aiko Mijin ku Annabin Rahma ya ba wa Mata ‘yancin
su a yayin da su ke tafiya tsirara, ku tuna da ayoyin da ake saukarwa Annabin
yayin da yake dakunan ku, sai dai ku ga fuskarsa ta canza jikinsa ya canza. Wanda
kuma ba matan Manzon Allah ba fa? Lallai ana karanta Kur’ani a dakunan Mata
suna sauraro, don haka Kur’ani ya shiga ko wani daki, ko wane kauye, sabpda
haka ku yi koyi da Matan Manzon Allah don inuwa daya ta tara mu duka, ita ce Al-
Kur’ani mai girma.
Lallai
a daina bayyana tufafi, ko kawa, ko ado, ko kuma jiki ga mjin da muharrami ba. Kur’ani
ya hana mata fita sai da lalura wanda shari’ah ta yarda da shi, amma fita haka
kawai babu dalili, Kur’ani ya hana ki, lallai Kur’ani ya tsawatar ga mata da su
zama masu kula da mutuncinsu, su yi tsayin-daka a kan hakkin Allah, da na
Mazajensu. Su ji tsoron Allah, idan har an fadawa Matan Manzon Allah haka, to
ina ga Matan wadansu wanda ba na Annabi ba, kasancewar ba su da fahimata irin
na matan Manzon Allah da karancin Imani saboda haka su suka fi cancanta ayi
masu wannan wa’azin.
‘Yanuwa
yana daga cikin munanan abubuwan da muke gani a cikin wannan kasa, da garuruwa,
da lunguna shine ka ga mace ta fita Matar Musulmi ta fita zuwa kasuwanni haka
kawai, ba gaira babu dalili, musamman kusantowar azumin nan; mata su je su cika
kasuwa, babu hijabi, ka ga mata a titi, su na siye suna sayarwa, babu hijabi
tattare da su. Musulunci bai hana ki zuwa kasuwa ba amma sai da dalili, sai kim
sa tufafi kuma sai kin dauki izini daga Mijinki, ko kuma daga Mahaifin ki, ko
kuma Waliyyin ki. ‘Yanuwa Wallahi wannan al’amari ya cika Kasa ya cika Garuruwa.
Ka ga mahaukaci yana tafiya tsirara, kaga kuma mai hankali a cikin mata ita ma
tana tafiya tsirara. Mumini da Fasiki, da Maihakali, da Wawa, da Mara hankali
yayi ta kallon tsiraicinta, bata damu ba, saboda rashin tsoron Allh da kiyaye
dokokin Allah, da kuma ganin cewa ai ba ita kadai bace. Allah ya rufeta da wani
Hijabi amma ta kware shi, ta bude shi, ta fito tsirara cikin kasuwa, akan
kwalta da titi ba su jin kunya, ko kuma cikin makarantu, daga cikin makarantu
wanda muke da su manya-manya, kai har da Sakandare, mara hankali yayi farin ciki,
mai hankali yayi bakin ciki.
‘Yanuwa
ku sani cewa wulakanta mace ne ta fito tsirara, wato shi ne ta fito babu
hjiabi, haduwar maza da mata a ko wanu
mataki, yana daga cikin abubuwan da ke sa Allah yayi fushi hakan yana fusata
Allah, kuma abu ne wanda Allah ya
haramata. Hijabi, wajibi ne a musulunci, yan uwa wanda suka zauna da manzon
Allah su ne suka ga yadda mata su ke sa hijabi a lokacin manzon Allah, saboda
haka ba ka da wata fassara face daga Manzon Allah, babu wani Malami da zai ce
ai sa gyale ya wadatar.
Ya
ku masu Mata, ya ku masu ‘Ya’ya ku sani cewa fitan Matanku tsirara yana kawo
matsala a Kasa, ku sani cewa duk Musulmi
mai kishi bai kamata ya bari shaidan yayi wasa da hankalin sa ba, bai kamata yayi
wasa da shari’ah ba, kada ka bari ayi wasa da hankalin ka da wasu fassarori, da
wasu ‘yan yaudara irin na shaidan, domin wannan na iya sa Allah yayi fushi da
kai da matarka, da dukiyar ka. Ka sani cewa Annabi ya nuna mana cewa karshe shi
ne nasara, idan karshen ka ya munana, na matanka su ka munana, an yi mummunan
karshe!
Saboda
haka kowa ya sa Iyalin sa su sa Hijabi, Annabin Rahama na cewa “Ko dai kuyi
umarni da kyakkyawan aiki, kuma ku yi hani da mummuna, ko kuma Allah ya kusa ya
saukar da wata bala’i mai girma”. ‘Yan uwa mu ji tsoron Allah lallai wanda ke
karkashin mu na iyalin mu, mu tabbata cewa sun sanya Hijabi, lallai wasu daga
cikin mutane sukan fadi cewa ga wasu sun sanya Hijabi amma suna sabon allah,
kuma ga wasu wanda basu sa hijabi ba amma suna biyayya ga Allah, to duka sai
ayi masu wa’azi Huduba tana kira cewa mai sa Hijabi ya cigaba da sawa amma ya ji
tsoron Allah, ka da ace ka bar gemu kuma kana cuta, ka dage wando kuma kana
yaudara, ka zama Ustaz amma mayaudari.
Akwai
wani hadisi mai abintsoro wanda Abu Huraira ya ruwaito cewa, “Iri biyu (2) na Mutane
su na daga cikin ‘yan wuta, Annabi yace shi bai gan su ba, amma za su zo a
karshen zamani; Akwai jama’a wanda suke da bulala kamar kunnuwan sa su na dukan
mutane ba gaira ba dalili” Sai ka yi bincike wasu mutane ne wanda suke dukan
mutane hakanan? “Annabi yace kuma da wasu mata, ga su da tufafi amma tsirara su
ke, sun tara gashi kamar tozan rakumi wanda yayi shekara uku, ba za su shiga
aljanna ba, kuma ba za su ji kamshin aljanna ba” ‘Yan uwa watau ashe mata, da
‘Ya’ya, da Dalibai, da su ke fito da kan su da tarin gashi, ga ta tsirara kuma
‘Ya Musulma. Allah kuma yace: “Ku kiyaye kawunanku da iyalanku daga wuta wanda
yake mutane da duwatsu sune makamashin ta. A cikin wutan akwai Mala’iku masu
tsanani, masu fushi, su na azaba ne kawai!” Allah ya kiyaye mu daga shiga wuta,
Allah ka kare mu daga sharrin kan mu, ka kare mu daga sharrin wanda mu ka kawo Duniya!
Huduba
ta biyu; bayan godiya ga Allah tana cewa ku ji tsoron Allah mai girma, ku
kasance masu da’a gare Shi, ku kasance masu biyyaya gare Shi. Mata su kasance
masu koyi da musulmai ba da Kafirai ba, su Kafirai Makiya Annabi ne, za kaga
mata sun bude kirjin su a waje, wuyanta a waje, ana ganin kafadar ra, wannan
bala’i ne, so ake ace Annabin mu bai iya ba. Ku sani cewa su ne irin wannan
matan da Annabi yace bai gani ba a lokacin sa amma za su zo nan gaba. Lallai
Kafirai sun ce ba za su rabu damu ba, sai sun rabamu da Annabi Muhammad SAW, mu
kuma mu rike koyarwar Manzon Allah, mu sanya tufafi irin wanda allah yake so.
Akwai bakin ciki a yau a ga cewa mu na koyi da Shaidan, mu na koyi da tufafi
wanda ba namu ba, ka ga Musulmi na cin abinci da hannun hagu, yana barin akaifa
tayi tsawo, yana barin gashin baki wai don ya ba mutane tsoro, ka ga namiji na
gaisawa da mace, Allah ka kare mu daga wannan bala’i, ku sani Manzon Allah yace
duk wanda yayi kama da wani zai tashi da shi Ranar tashin Alkiyama.
‘Yan
uwa mu kiyaye koyi da Yahudu, mu yi koyi da Manzon Allah, wannan kadan kenan
daga cikin karantarwar Kur’ani da karantarwar manzon Allah SAW. Lallai wani Malami
yayi bayani mai dadi lokacin da aka zo yin taro na Sarauniyar kyau a Najeriya,
ya nuna cewa kamar kwai ne wanda aka bare da wanda ba’a bare ba, shin wanne za ka
zaba? Tabbas wanda ba’a bare ba! Wai shin tsarin kafirai ko na jahiliyya kuke
so, ko tsarin musulunci? Ya Allah mun tuba, lallai mace ta karrama kan ta idan
tasa tufafi irin na musulunci, sannan ta raba kanta da dabbobi. Za ku ga
kafirai suna fitowa tsirara a gaban mazajen su saboda haka Allah ya tsine masu.
Ibn Al-Qayyin yace duk jikin da ake rufe shi sai kaga yafi jikin da ba’a rufewa
lafiya da kyau.
Muna
rokon Allah ya shiryar da al’umman annabi Muhammad SAW, kuma idan an hana ki
sanya hijabi wajen aiki, babu komai kije kiyi aikin ki, idan ta fito ki sa
hijabin kuma ki sake shi har kasa, wata rana wadanda su ke hana tan Allah zai
canza su, zai kawo wanda za suce a sa. Kuma muna kira ga Shugabanni wanda su ke
da ikon bari a sa hijabi da su bari a sa din, idan ba haka ba Allah zai jarrabe
su da fitina. Allah yace kaji tsoron mutuwa!
Huduba
a karshe tana jawo hankalin malamai da su ke bada fatawa ba bisa yadda Manzon
Allah da Sahabbai suka tafi a kai ba, da su ji tsoron Allah, su koma su duba
littatafai, da yadda Sahabbai su ka fassara wannan al’amarin. Kuma lallai mata
ku ji tsoron Allah, gyale ki sa wa mijinki a gida ko ma ki fito masa tsirara.
Allah
muna rokonka ka daukaka musulunci, ya Allah yadda ka hada kafadun mu, Allah ka
hada zukatan mu a kan gaskiya, ya Allah ka kare mu daga dukkan fitina, Allah ka
sa mu zama masu gaskiya masu san gaskiya. Allah ka bamu nasara. Ameen!